Muhimman abubuwa 11 da ya dace ku sani game da Ajimobi

Muhimman abubuwa 11 da ya dace ku sani game da Ajimobi

Tsohon gwamna kuma Sanata na jihar Oyo, Abiola Ajimobi ya rasu a ranar Alhamis 25 ga watan Yunin shekarar 2020 sakamakon cutar COVID-19 wato coronavirus.

Ga wasu muhimman abubuwa 11 da ya kamata ka sani game da Abiola Ajimobi kamar yadda The Nation ta wallafa.

Muhimman abubuwa 11 da ya dace ku sani game da Ajimobi
Muhimman abubuwa 11 da ya dace ku sani game da Ajimobi. Hoto daga BBC
Asali: UGC

1. An haifi Abiola Ajimobi ne a ranar 16 ga watan Disamban shekarar 1949 a Oja-Iba a Ibadan.

2. Kakansa basarake na Sobaloju na Ibadan. Mahaifinsa, Pa Ajimobi, shima dan majalisa ne a tsohuwar shiyar Yamma kuma kawunsa, Hon. N.A. Ajimobi tsohon ministan Ayyuka da Sufuri ne a shiyar ta Yamma.

3. Yayi karatunsa na frimari a Saint Patricks School, Oke-Padre kuma ya kammala frimari a City Council Primary School Aperin.

Ya yi karatun sakandare a Lagelu Grammar School. Yana cikin dalibai masu hazaka wurin wasanni kamar kwallon kafa, guje-guje da sauransu.

4. Ajimobi ya yi karatun digiri na farko a State University of New York a Buffalo a Amurka. Ya yi digirinsa na biyu a Governors State University, Illinois.

5. Ajimobi ya auri Florence Ajimobi a shekarar 1980 kuma sun haifi yara biyar. Diyarsa ta farko Abisola Kola-Daisi 'yar kasuwa ce wacce ta kafa kamfanin Florence H Luxury.

6. A 2003, Ajimobi ya zama Sanata a Najeriya. Ya rike mukamin mataimakin shugaban marasa rinjaye.

DUBA WANNAN: Hamshakin biloniyan Najeriya ya shirya angwancewa da diyar Trump

A 2007, ya yi takarar gwamna a karkashin jam'iyyar APC amma bai yi nasara ba. Ya sake takara a 2011 a karkashin jam'iyyar ACN kuma ya lashe zabe.

7. Ya sake yin takarar gwamna karo na biyu a Afrilun 2015 a karkashin jam'iyyar APC inda ya yi nasara. Ajimobi shine gwamna na farko da ya fara yin tazarce a jihar.

8. An zabi Ajimobi a matsayin sanata a karkashin jam'iyyar APC a ranar 28 ga watan Satumban 2018 inda ya wakilci Oyo mazabar Oyo ta Kudu.

9. A ranar 9 ga watan Maris ne 2019, Ajimobi ya rasa kujerarsa ta sanata inda ya sha kaye hannun Kola Balogun na jam'iyyar PDP.

10. A ranar 17 ga watan Yunin 2020, Kwamitin Gudarwa, NWC na jam'iyyar APC ta zabi Ajimobi a matsayin shugaban riko na jam'iyyar.

11. A ranar 18 ga watan Yunin 2020, an yada jita-jita cewa Ajimobi ya rasu amma daga bisani aka gano ba gaskiya bane.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel