Yanzu: Yan majalisar dokokin jihar Imo 13 sun kamu da cutar Coronavirus

Yanzu: Yan majalisar dokokin jihar Imo 13 sun kamu da cutar Coronavirus

- Annobar cutar COVID-19 ta kai simame majalisar dokokin jihar Imo

- Akalla mambobin majalisar 13 sun kamu da cutar

Hankula sun tashi a jihar Imo yayinda mambobin majalisar dokokin jihar 13 suka kamu da cutar nan mai toshe numafashi wato Coronavirus, rahoton Channels TV ya bayyana.

Wannan ya bayyana ne kwanaki shida bayan dan majalisan farko ya kamu da cutar amma aka ki bayyana sunansa.

Shugaban kwamitin yaki da COVID-19 a jihar, Farfesa Maurice Iwu, ya bayyana ranar Talata, 16 ga Yuni cewa dan majalisan ya kamu da cutar.

Ya ce an killace dan majalisan da iyalinsa kuma an baiwa dukkan sauran mambobin majalisar umurnin suyi gwajin cutar.

Yayinda yake magana da manema labarai a birnin Owerri, Farfesa Iwu ya kara cewa wata mai jego wacce ta kamu da cutar ta mutu bayan haifan yan biyu cikin lafiya.

Bisa alkaluman hukumar hana yaduwar cututtuka a Najeriya, jimillan mutane 243 suka kamu da cutar a jihar Imo.

Yanzu: Yan majalisar dokokin jihar Imo 13 sun kamu da cutar Coronavirus
Yanzu: Yan majalisar dokokin jihar Imo 13 sun kamu da cutar Coronavirus
Asali: Twitter

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng

Tags: