Karin mutum 661 sun kamu da korona a Najeriya

Karin mutum 661 sun kamu da korona a Najeriya

Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa a Kasa (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 661 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11.29 na daren ranar Asabar 20 ga Yuni na shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na dandalin sada zumunta na Twitter, ta ce karin karin mutune 661 da suka kamu sun fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

Da dumi-dumi: Karin mutum 661 sun kamu da korona a Najeriya
Da dumi-dumi: Karin mutum 661 sun kamu da korona a Najeriya
Asali: Twitter

Lagos-230

Rivers-127

Delta-83

FCT-60

Oyo-51

DUBA WANNAN: Kalli bidiyon yadda sojoji suka yi wa 'yan ta'adda 'ruwan wuta' a matattaransu da ke Bula Korege

Edo-31

Bayelsa-27

Kaduna-25

Plateau-13

Ondo-6

Nasarawa-3

Ekiti-2

Kano-2

Borno-1

Alkalluman da hukumar ta dakile cututtukan ta fitar a ranar Asabar 20 ga Yunin shekarar 2020 ya nuna cewa jumullar wadanda suka kamu da cutar ta korona a kasar 19,808.

An sallami mutum 6718 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jumullar mutum 506.

A wani labarin daban, kun ji dan majalisar jihar Enugu mai wakiltan mazabar Isa-uzo, Chijioke Ugwuwze ya riga mu gidan gaskiya kamar yadda rahotanni suka bayyana.

Marigayin ya rasu ne sakamakon bugun zuciya kamar yadda kaninsa, Ejike ya tabbatar a ranar Asabar 20 ga watan Yunin 2020 kamar yadda Legit.ng ta ruwaito.

Dan uwan marigayin ya bayyana cewa Ugwueze ya mutu yana da shekaru 49 a duniya kuma ya dade yana fama da ciwon hawan jini kamar yadda kamfanin dillancin labarai, NAN, ta ruwaito.

Dan uwansa ya kara da cewa dan majalisar ya mutu ne a asibitin koyarwa da ke na Enugu da ke Parklane a yammacin ranar Juma'a 19 ga watan Yuni.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164