Karin mutum 661 sun kamu da korona a Najeriya

Karin mutum 661 sun kamu da korona a Najeriya

Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa a Kasa (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 661 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11.29 na daren ranar Asabar 20 ga Yuni na shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na dandalin sada zumunta na Twitter, ta ce karin karin mutune 661 da suka kamu sun fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

Da dumi-dumi: Karin mutum 661 sun kamu da korona a Najeriya
Da dumi-dumi: Karin mutum 661 sun kamu da korona a Najeriya
Asali: Twitter

Lagos-230

Rivers-127

Delta-83

FCT-60

Oyo-51

DUBA WANNAN: Kalli bidiyon yadda sojoji suka yi wa 'yan ta'adda 'ruwan wuta' a matattaransu da ke Bula Korege

Edo-31

Bayelsa-27

Kaduna-25

Plateau-13

Ondo-6

Nasarawa-3

Ekiti-2

Kano-2

Borno-1

Alkalluman da hukumar ta dakile cututtukan ta fitar a ranar Asabar 20 ga Yunin shekarar 2020 ya nuna cewa jumullar wadanda suka kamu da cutar ta korona a kasar 19,808.

An sallami mutum 6718 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jumullar mutum 506.

A wani labarin daban, kun ji dan majalisar jihar Enugu mai wakiltan mazabar Isa-uzo, Chijioke Ugwuwze ya riga mu gidan gaskiya kamar yadda rahotanni suka bayyana.

Marigayin ya rasu ne sakamakon bugun zuciya kamar yadda kaninsa, Ejike ya tabbatar a ranar Asabar 20 ga watan Yunin 2020 kamar yadda Legit.ng ta ruwaito.

Dan uwan marigayin ya bayyana cewa Ugwueze ya mutu yana da shekaru 49 a duniya kuma ya dade yana fama da ciwon hawan jini kamar yadda kamfanin dillancin labarai, NAN, ta ruwaito.

Dan uwansa ya kara da cewa dan majalisar ya mutu ne a asibitin koyarwa da ke na Enugu da ke Parklane a yammacin ranar Juma'a 19 ga watan Yuni.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel