Karin mutum 573 sun kamu da korona a Najeriya, jimilla 16,658

Karin mutum 573 sun kamu da korona a Najeriya, jimilla 16,658

Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa a Kasa (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 573 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11.50 na daren ranar Litinin 15 ga Yuni na shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 573 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

Lagos-216

Rivers-103

Oyo-68

Edo-40

Kano-21

Gombe-20

FCT-17

Delta-13

DUBA WANNAN: 'Da yardarsu muke saduwa', inji magidancin da ke zina da 'ya'yansa mata biyu

Plateau-12

Bauchi-12

Niger-10

Kebbi-9

Ogun-8

Ondo-8

Abia-7

Nasarawa-5

Borno-1

Kwara-1

Benue-1

Anambra-1

Alkalluman da hukumar ta dakile cututtukan ta fitar a ranar Litinin 15 ga Yunin shekarar 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu da cutar ta korona a kasar 16,658.

An sallami mutum 5,349 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 424.

A wani labarin daban kunji gwamnatin jihar Kaduna ta bayar da umarnin janye dukkan wani shinge da aka saka a iyakokin shiga jihar tare da bayar da umarnin maye gurbinsu da wasu sabbi don cigaba da tabbatar da dokar hana bulaguro a tsakanin jihohi.

A cikin wani jawabi da Muyiwa Adekeye, mai taimakawa gwamna a bangaren yada labarai da sadarwa, ya fitar, gwamnatin Kaduna ta sanar da dakatar da aikin dukkan kwamitin da aka kafa don tsaron kan iyakokin jihar.

A cewar sanarwar, gwamnati ta dauki wannan mataki ne bisa shawarar da kwamitin yaki da annobar korona a jihar ya bayar.

Daga yanzu, shingen kan hanya da aka yarda dasu sune wadanda aka saka domin tabbatar da dokar takaita zirga-zirga a tsakanin karfe 8:00 na dare zuwa 5:00 na safe, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Gwamnatin ta kara da cewa ta samu rahotannin yadda jami'an tsaro da ke aiki a kan iyakoki suke tatsar kudi a hannun direbobi a wuraren da aka saka shingen hanya, lamarin da mahukunta a jihar Kaduna suka ce yana kara kawo dagulewar al'amura.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164