Karin mutum 573 sun kamu da korona a Najeriya, jimilla 16,658
Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa a Kasa (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 573 a fadin Najeriya.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11.50 na daren ranar Litinin 15 ga Yuni na shekarar 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 573 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;
Lagos-216
Rivers-103
Oyo-68
Edo-40
Kano-21
Gombe-20
FCT-17
Delta-13
DUBA WANNAN: 'Da yardarsu muke saduwa', inji magidancin da ke zina da 'ya'yansa mata biyu
Plateau-12
Bauchi-12
Niger-10
Kebbi-9
Ogun-8
Ondo-8
Abia-7
Nasarawa-5
Borno-1
Kwara-1
Benue-1
Anambra-1
Alkalluman da hukumar ta dakile cututtukan ta fitar a ranar Litinin 15 ga Yunin shekarar 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu da cutar ta korona a kasar 16,658.
An sallami mutum 5,349 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 424.
A wani labarin daban kunji gwamnatin jihar Kaduna ta bayar da umarnin janye dukkan wani shinge da aka saka a iyakokin shiga jihar tare da bayar da umarnin maye gurbinsu da wasu sabbi don cigaba da tabbatar da dokar hana bulaguro a tsakanin jihohi.
A cikin wani jawabi da Muyiwa Adekeye, mai taimakawa gwamna a bangaren yada labarai da sadarwa, ya fitar, gwamnatin Kaduna ta sanar da dakatar da aikin dukkan kwamitin da aka kafa don tsaron kan iyakokin jihar.
A cewar sanarwar, gwamnati ta dauki wannan mataki ne bisa shawarar da kwamitin yaki da annobar korona a jihar ya bayar.
Daga yanzu, shingen kan hanya da aka yarda dasu sune wadanda aka saka domin tabbatar da dokar takaita zirga-zirga a tsakanin karfe 8:00 na dare zuwa 5:00 na safe, kamar yadda sanarwar ta bayyana.
Gwamnatin ta kara da cewa ta samu rahotannin yadda jami'an tsaro da ke aiki a kan iyakoki suke tatsar kudi a hannun direbobi a wuraren da aka saka shingen hanya, lamarin da mahukunta a jihar Kaduna suka ce yana kara kawo dagulewar al'amura.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng