An samu karin masu korona 501 a Najeriya, jimilla 15,682

An samu karin masu korona 501 a Najeriya, jimilla 15,682

Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa a Kasa (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 501 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11.42 na daren ranar Asabar 13 ga Yuni na shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 501 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

Lagos-195

FCT-50

Kano-42

Kaduna-27

Edo-26

Oyo-22

Imo-21

Gombe-17

Benue-12

DUBA WANNAN: Da ɗumi-ɗumi: 'Yan bindiga sun sake kashe wani basarake a Katsina

Enugu-12

Delta-11

Anambra-11

Ebonyi-10

Nasarawa-9

Ogun-9

Bauchi-8

Kebbi-4

Akwa Ibom-3

Jigawa-3

Katsina-3

Yobe-2

Borno-2

Kwara-1

Ondo-1

Alkalluman da hukumar ta dakile cututtukan ta fitar a ranar Asabar 13 ga Yunin shekarar 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu da cutar ta korona a kasar 15682.

An sallami mutum 5101 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 407.

A wani labarin da Legit.ng ta wallafa, kun ji mazauna garin Zaria a ranar Juma'a sunyi murnar bude masallatan Juma'a a birnin Zazzau da wasu garurruwa da ke jihar ta Kaduna.

Tun misalin karfe 8 na safe ne mutane da dama suka yi wanka suka saka kayatattun kayansu domin shirin zuwa salla a masallatan Juma'a da suke raayin zuwa kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Kazalika wasu daga cikin masallatan suna kiyaye dokokin da hukumomin lafiya suka bayar da shawawarin a rika kiyaye wa domin dakile yaduwar cutar coronavirus.

Wani mazaunin Zaria, Malam Ibrahim Danllami ya ce mafi yawancin yara a birnin ta Zazzau sun dauki Juma'ar ta jiya tamkar ranar Sallar Idi ne a wurinsu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164