An samu karin masu korona 501 a Najeriya, jimilla 15,682

An samu karin masu korona 501 a Najeriya, jimilla 15,682

Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa a Kasa (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 501 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11.42 na daren ranar Asabar 13 ga Yuni na shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 501 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

Lagos-195

FCT-50

Kano-42

Kaduna-27

Edo-26

Oyo-22

Imo-21

Gombe-17

Benue-12

DUBA WANNAN: Da ɗumi-ɗumi: 'Yan bindiga sun sake kashe wani basarake a Katsina

Enugu-12

Delta-11

Anambra-11

Ebonyi-10

Nasarawa-9

Ogun-9

Bauchi-8

Kebbi-4

Akwa Ibom-3

Jigawa-3

Katsina-3

Yobe-2

Borno-2

Kwara-1

Ondo-1

Alkalluman da hukumar ta dakile cututtukan ta fitar a ranar Asabar 13 ga Yunin shekarar 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu da cutar ta korona a kasar 15682.

An sallami mutum 5101 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 407.

A wani labarin da Legit.ng ta wallafa, kun ji mazauna garin Zaria a ranar Juma'a sunyi murnar bude masallatan Juma'a a birnin Zazzau da wasu garurruwa da ke jihar ta Kaduna.

Tun misalin karfe 8 na safe ne mutane da dama suka yi wanka suka saka kayatattun kayansu domin shirin zuwa salla a masallatan Juma'a da suke raayin zuwa kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Kazalika wasu daga cikin masallatan suna kiyaye dokokin da hukumomin lafiya suka bayar da shawawarin a rika kiyaye wa domin dakile yaduwar cutar coronavirus.

Wani mazaunin Zaria, Malam Ibrahim Danllami ya ce mafi yawancin yara a birnin ta Zazzau sun dauki Juma'ar ta jiya tamkar ranar Sallar Idi ne a wurinsu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel