Da duminsa: Majalisar dattawa ta tabbatar da sabbin jakadu 42 (Jerin sunayensu)

Da duminsa: Majalisar dattawa ta tabbatar da sabbin jakadu 42 (Jerin sunayensu)

Majalisar dattawa a ranar Alhamis ta amince da mutane 42 da shugaban Buhari ya zaba matsayin sabbin jakadun Najeriya zuwa kasashen waje.

Hakazalika majalisar ta amince da nadin Justice Monica Dongban-Mensem a matsayin shugabar kotun daukaka kara da kuma James Kolo matsayin kwamishana a hukumar FCC.

Tabbatar da su ya biyo bayan rahoton kwamitin Sanata Adamu Bulkachuwa wanda shine shugaban kwamitin harkokin waje a majalisar dattawa.

Za ku tuna cewa shugaba Muhammadu Buhari ya aike da sunayen mutane 42 da ya zaba matsayin jakadun Najeriya.

Da duminsa: Majalisar dattawa ta tabbatar da sabbin jakadu 42 (Jerin sunayensu)
Majalisar dattawa
Asali: UGC

KU KARANTA: Shugaba Buhari zai yiwa yan Najeriya jawabi ranar Juma'a

Ga jerin sunayen wadanda aka tabbatar:

Innocent Alaoma Iwejuo

Aishatu Aliyu Iwejuo

Mukhtar Ibrahim Bashir

Chikezie Ogbonna Nwachukwu

Alex Enan Kefas

Gabriel Mustapha Okoko

Aisha Mohammed Garba

Asari Edem Allotey (Mrs.)

George Ehidiamen Edokpa, Esq

Adamu Ibrahim Lamuwa

Abubakar Mohammed Sarki

Yakubu Abdullahi Ahmed

Suleiman Dauda Umar

Gambo Yusuf Hamza

Nura Abba Rimi

Mfawa Omini Abam

Lami Sauda Remawa-Ahmed

Mohammed Manu

Ingekem Regina Ocheni (Mrs.)

Ismaila Yusuf Abba

Mistura Abdulraheem (Mrs.)

Wosilat Abimbola Adedeji

Obinna Cheedu Onowu

Ekpebike Steve Agnana

Ogah Usman Ari

Safiu Olukayode Olaniyan

Abidoun Richards Adejola

Olawale Emmanuel Awe

Ibim Nkem Charles

Zachariah Mallam Ifu

Raymond Udoffe Brown

Godfrey A. E. Odudigbo

Ahmed Sule

Olukayode O. Aluko

Victor Adekunle Adeleke, Esq

Matin Senkom Adamu

Bukar Buni Hamman

Anderson Nkemakonam Mabubike

Nart Augustine Kolo,

Ismail Ayobami Alatishe

Yakubu Santuraki Suleiman

Benaoyagha Bernard Mese Okoyen

A bangare guda, Legit ta ruwaito muku cewa Majalisar dattawa ta yi barazanar bayar da sammacin kama Ministan Labarai da Al’adu; Alhaji Lai Mohammed, Karamin Ministan Man Fetur; Timipre Sylva da kuma Ministan Wuta; Engr. Saleh Mamman.

Majalisar ta ce za ta bayar da sammacin cafke ministocin uku saboda sun ki amsa goron gayyatar da ta ba su na neman su yi bayani a kan duk wani shige-da-fice na batar da kudi a ma'aikatunsu.

Shugaban kwamitin kula da kudin al'umma a majalisar, Sanata Matthew Urhoghide na jam'iyyar PDP mai wakiltar shiyar Edo ta Kudu, shi ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel