Karin mutum 241 sun harbu da korona a Najeriya, jimilla 10819

Karin mutum 241 sun harbu da korona a Najeriya, jimilla 10819

Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa a Kasa (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 241 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11.52 na daren ranar Talata, 2 ga watan Yuni na shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 241 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

Lagos-142

Oyo-15

FCT-13

Kano-12

Edo-11

Delta-10

DUBA WANNAN: Kotu ta tsare mutumin da ya yi zina da surukarsa

Kaduna -9

Rivers-9

Borno-8

Jigawa-4

Gombe-3

Plateau-3

Osun-1

Bauchi-1

Alkalluman da hukumar ta NCDC ta fitar a ranar Talata 2 ga watan Yunin 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu ta cutar ta korona a kasar 10819.

An sallami mutum 3239 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 314.

A wani labari na daban, wasu 'yan bindiga da ba san ko su wanene ba sun harbe hakimin 'Yantumaki har lahira a jihar Katsina, Abubakar Atiku Maidabino a fadarsa a safiyar ranar Litinin.

Wata majiya daga garin ta shaidawa Daily Trust cewa 'yan bindigan sun taho a babura ne misalin karfe 12 na dare inda suka rika harbe harbe a iska domin razana mutanen kauyen.

Daga bisani yan bindigan sun shiga cikin fadar suka kashe hakimin nan take kuma suka raunata daya daga cikin masu gadinsa.

Za a yi janai'zar mammacin misalin karfe 11 na safe a fadarsa bisa koyarwan addinin musulunci.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164