Jerin kananan hukumomi 20 da akafi yawan masu cutar Korona a Najeriya

Jerin kananan hukumomi 20 da akafi yawan masu cutar Korona a Najeriya

- Hukumar NCDC ta sakin jerin kananan hukumomin da suka fi yawan masu cutar Coronavirus a Najeriya

- A jerin, kananan hukumomin nan 20 ne kashe 60 cikin 100 na masu cutar suke zaune

- 11 cikin wadannan kananan hukumomin na Jihar Legas

Hukumar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya, NCDC, ta saki jerin kananan hukumomin da suka yawan masu dauke da cutar Coronavirus a Najeriya.

The Nation ta ruwaito cewa lissafin fa NCDC ta saki ya nuna cewa wadannan kananan hukumomin 20 ke dauke da kashi 60% na masu cutar Korona a Najeriya.

Najeriya na da kananan hukumomi 774.

Legit.ng ta tattaro cewa 11 cikin wadannan kananan hukumomin na jihar Legas.

KU KARANTA: Yadda aka samu shugabannin kasa 2, gwamnoni 4 da ministoci 2 a aji daya

Ga jerin kananan hukumomi 20 mafi yawan masu cutar COVID-19 a Najeriya:

1. Lagos Mainland council - 1,274

2. Abuja Municipal council - 536

3. Mushin LGA (Lagos) - 458

4. Eti-Osa LGA (Lagos) - 403

5. Tarauni LGA (Kano) - 248

6. Katsina LGA - 242

7. Alimosho LGA (Lagos) - 239

8. Kosofe (Lagos) - 175

9. Dutse (Jigawa) - 170

10. Ikeja (Lagos) - 168)

11. Maiduguri (Borno) - 167

12. Nassarawa - 152,

13. Oshodi/Isolo (Lagos) - 132

14. Apapa (Lagos) - 131

15. Amuwo Odofin (Lagos) - 129

16. Oredo (Edo ) - 126

17. Kwaryar Bauchi - 114

18. Lagos Island - 111

19. Surulere (Lagos) - 110

20. Ado Odo/Ota (Ogun) - 107

A ranar Asabar, 30 ga watan Mayu, an gwada samfurin mutane 62,583 kuma 10,023 aka samu da cutar.

A cewar rahoton, ba'a samu tabbacin yadda mutane 7,726 suka kamu da cutar ba, hakan na nuna cewa cutar ta yi mumunar yaduwa cikin al'umma.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng