Karin mutum 416 sun harbu da korona a Najeriya, jimilla 10578
Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa a Kasa (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 416 a fadin Najeriya.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11.52 na daren ranar Litinin, 1 ga watan Yuni na shekarar 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 416 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;
Lagos-192
Edo-41
Rivers-33
Kaduna-30
Kwara-23
Nasarawa-18
Borno-17
DUBA WANNAN: Jerin sunayen sabbin direktoci 6 da Buhari ya nada a NNPC
FCT-14
Oyo-10
Katsina-7
Abia-5
Delta-5
Adamawa-4
Kano-4
Imo-3
Ondo-3
Benue-2
Bauchi-2
Ogun-2
Niger-1
Alkalluman da hukumar ta NCDC ta fitar a ranar Litinin 1 ga watan Yunin 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu ta cutar ta korona a kasar 10578.
An sallami mutum 3122 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 299.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng