Karin mutum 416 sun harbu da korona a Najeriya, jimilla 10578

Karin mutum 416 sun harbu da korona a Najeriya, jimilla 10578

Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa a Kasa (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 416 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11.52 na daren ranar Litinin, 1 ga watan Yuni na shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 416 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

Lagos-192

Edo-41

Rivers-33

Kaduna-30

Kwara-23

Nasarawa-18

Borno-17

DUBA WANNAN: Jerin sunayen sabbin direktoci 6 da Buhari ya nada a NNPC

FCT-14

Oyo-10

Katsina-7

Abia-5

Delta-5

Adamawa-4

Kano-4

Imo-3

Ondo-3

Benue-2

Bauchi-2

Ogun-2

Niger-1

Alkalluman da hukumar ta NCDC ta fitar a ranar Litinin 1 ga watan Yunin 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu ta cutar ta korona a kasar 10578.

An sallami mutum 3122 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 299.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164