Covid-19: Sabbin mutum 226 sun kamu a Najeriya, jimilla 6401

Covid-19: Sabbin mutum 226 sun kamu a Najeriya, jimilla 6401

Sabbin alkalluma da hukumar dakile cututtuka masu yaduwa a Najeriya, NCDC ta fitar a daren Talata sun nuna cewa masu dauke da korona yanzu haka a kasar sun kai 6,401.

Hakan ya biyo bayan samun karin sabbin mutum 226 da suka sake kamuwa da cutar a cikin sa'o'i 24 da suka shude.

Hukumar ta wallafa alakallumar ne a shafinsa na dandalin sada zumunta na Twitter kamar yadda ta saba a kullum.

Yanzu dai jimilar wadanda da cutar ta kashe a fadin kasar ya kai 192, yayin da mutum 1,734 suka warke kuma aka sallamesu.

A Legas, jihar da ta fi yawan masu fama da Covid-19, sabbin alkaluma sun nuna an sake samun mutane 131 da suka harbu.

Jihar Ogun ita ce ta biyu a jadawalin daren Talata da mutane 25 sabbin kamu.

Sai Plateau mai 15, Edo 11, Kaduna 7, Oyo 6, Abuja da Adamawa kowannensu 5.

Jigawa, Ebonyi da Borno kowannensu mutum 4 sai Nasarawa an samu sabbin mutum 3.

Gombe da Bauchi an samu mutum 2,2 sai Enugu da Bayelsa kowannensu 1,1.

DUBA WANNAN: Daya daga cikin mambobin FCC 37 da Buhari ya nada ya mutu kafin rantsar da su

A wani labarin, kun ji cewa wata mata mai shekaru 22 cikin wadanda suke jinyar COVID-19 a Legas ta haifi tagwaye a Asibitin Koyarwa ta Jamiar Legas (LUTH).

Mai jinyar ta haifi mace da na miji a ranar Talata 19 ga watan Mayu, hakan ya kawo jimillar jariran da aka haifa a asibitin zuwa hudu.

Asibitin ya tabbatar da haihuwar tagwayen cikin sakon da ya wallafa a shafinsa na dandalin sada zumunta ta Twitter.

Sakon ya ce, "Tawagar likitoci a LUTH da masu kula da numfashi da jamian jinyan a yau Talata, 19 ga watan Mayun 2020 sun taimakawa wata mata mai shekaru 22 da ke dauke da COVID-19 ta haifi tagwaye mace da na miji.

"Nauyin jariran a lokacin da aka haife su kilogram 3.2 na miji sai macen kilogram 3.25, matar ta haihu ne ta hanyar tiyata. "Mahaifiyar da jariran duk suna cikin koshin lafiya!”.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa.Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164