Kashi 51% na duk masu cutar korona sun kasance a kananan hukumomi 9 na Najeriya - Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, kashi 51 cikin 100 na duk adadin masu cutar korona a Najeriya sun kasance a wasu kananan hukumomi 9 kacal da ke fadin kasar.
Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha, shi ne ya sanar da hakan da cewa kananan hukumomi 9 a Najeriya sun tattare kashi 51 cikin 100 na duk masu cutar korona a kasar.
Sanarwar Sakataren Gwamnatin ta zo ne a ranar Litinin yayin ganawa da manema labarai kan halin da kasar ta ke ciki game da annobar korona.
Boss Mustapha wanda ya kasance shugaban kwamitin kula da annobar korona a Najeriya, ya ce bincikensu ya gano cewa, wasu kananan hukumomi 9 a fadin Najeriya sun dauke nauyin duk wani adadi na masu cutar korona a kasar.
Yayin tabbatar da cewa kananan hukumomin 9 suna da kashi 51% na adadin masu cutar korona a duk fadin Najeriya, ya kuma ce dukkaninsu na da dimbin al'umma mai yawan gaske.
Ya kuma lura cewa an inganta tsarin kiwon lafiya da kayan aiki don lalube da gwaji, gami da killace wadanda cutar korona ta harba.
KARANTA KUMA: An yi gwajin sabon maganin cutar korona a kan mutane 45
Haka kuma Hukumar yaki da cututtuka masu yaduwa a kasa (NCDC), ta sanar da cewa karin sabbin mutane 216 ne aka tabbatar da sun kamu da kwayar cutar covid-19 a fadin Najeriya.
A cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin 11:53 na daren ranar Litinin a shafinta na Twitter, ta ce an samu karin sabbin mutane 216 da suka kamu a wasu jihohi goma na Najeriya
NCDC ta fitar da jerin jihohi da jimillar sabbin wadanda cutar ta harba a kowacce jiha kamar haka: 74-Lagos, 33-Katsina, 19-Oyo, 17-Kano, 13-Edo, 10-Zamfara, 8-Ogun, 8-Gombe, 8-Borno, 7-Bauchi, 7-Kwara, 4-FCT, 3-Kaduna, 3-Enugu, 2-Rivers.
A halin yanzu alkaluman NCDC sun tabbatar da cewa kawo yanzu, akwai jimillar mutane 6175 da aka tabbatar sun harbu da kwayoyin cutar korona a fadin kasar.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng