Yanzu-yanzu: Karin mutane 67 sun warke daga Coronavirus, an sallamesu

Yanzu-yanzu: Karin mutane 67 sun warke daga Coronavirus, an sallamesu

Ma'aikatar kiwon lafiyan jihar Legas ta sanar da warkewa da sallamar masu cutar Coronavirus 67 a jihar bayan gwaji biyu a jere ya nuna sun barranta daga cutar.

Ma'aikatar ta bayyana hakan ne a shafinta na Tuwita ranar Asabar, 16 ga wtaan Mayu, 2020.

A cewar jawabin, cikin wadanda aka sallama akwai Maza 45 da Mata 22 - wanda ya hada da yan kasar Indiya 2 da dan China 1.

Kawo yanzu, jihar Legas ta sallami mutane 608 masu fama da cutar Korona.

KU KARANTA: COVID-19: Sarkin Daura ya yi nasiha mai ratsa zuciya bayan samun waraka

Jawabin yace: "Masu jinyar cutar COVID19 67; mata 22 da maza45; harda yan kasar waje 3 - Indiyawa 2 da Bachine 1 sun samu sallama daga cibiyoyin killacewanmu."

A ranar 15 ga Mayu, mun samu mutuwar mutane 3. Yanzu adadin wadanda suka mutu sakamakon cutar COVID19 a Legas ya kai 36.

A yanzu adadin wadanda aka sallama ya hau 608."

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng