Yadda masu garkuwa da mutane suka tsere suka bar wadanda suka sace a daji

Yadda masu garkuwa da mutane suka tsere suka bar wadanda suka sace a daji

Masu garkuwa da mutane da suka kama wani soja mai mukamim Kyaftin mai suna Gana sun yi watsi da mutanen da suke garkuwa da su a cikin daji sun tsere.

Rahoto ya bayyana cewa masu garkuwa da mutanen sun tsere ne yayin da jamian tsaro suke daf da isowa mabuyarsu a cikin daji kamar yadda The Nation ta ruwaito.

Yan bindigan sun sace Gana da wasu mutanen ne a ranar Talata a kusa da garuruwan Auga-Akoko-Ibilo da ke kan iyakan jihohin Ondo da Edo.

Yadda masu garkuwa da mutane suka tsere suka bar wadanda suka sace a daji
Yadda masu garkuwa da mutane suka tsere suka bar wadanda suka sace a daji. Hoto daga The Nation
Asali: Twitter

An gano su ne a wani daji da ke Ibilo a jihar Edo.

DUBA WANNAN: JAMB: Jihohi 5 da ke kan gaba wajen magudin jarabawar 2020

Mai magana da yawun rundunar sojoji ta 32 Artillery Brigade a Akure, Kyaftin Ayorinde ya ce tawagar sojoji da wasu jamian tsaro ne suka ceto sojan ba tare da an biya kudin fansa.

A wani rahoton, mun kawo muku cewa Rundunar Yan sanda ta jihar Sokoto ta kama mutum 155 daga karfe 8 na daren ranar Laraba zuwa karfe 6 na ranar Alhamis da suka saba dokar kulle da aka saka a jihar don dakile yaduwar annobar COVID-19.

Wannan na cikin wata sanarwa ce ta mai magana da yawun rundunar, Muhammad Sadiq, mai mukamin mataimakin superintendent na yan sanda ya fitar a ranar Alhamis a Sokoto kamar yadda Premium Times ta ruwaito.

Mr Sadiq ya ce twagar hadin gwiwa ta jamian tsaro karkashin jagorancin kwamishinan Yan sandan jihar, Ibrahim Kaoje, daga ranar 5 ga watan Mayu zuwa 14 ga watan Mayu ta kama motoci da babura a kalla 63.

Ya ce, "An gudanar da ingattacen binciken a kan kamen da aka yi kamar yadda kwamishinan yan sanda ya bayar da umurni kafin a kai su kotu."

Ya bayyana cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wurin kama duk wani mutum ko kungiya ta aka samu da saba dokar ta hana fita.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel