Yadda masu garkuwa da mutane suka tsere suka bar wadanda suka sace a daji

Yadda masu garkuwa da mutane suka tsere suka bar wadanda suka sace a daji

Masu garkuwa da mutane da suka kama wani soja mai mukamim Kyaftin mai suna Gana sun yi watsi da mutanen da suke garkuwa da su a cikin daji sun tsere.

Rahoto ya bayyana cewa masu garkuwa da mutanen sun tsere ne yayin da jamian tsaro suke daf da isowa mabuyarsu a cikin daji kamar yadda The Nation ta ruwaito.

Yan bindigan sun sace Gana da wasu mutanen ne a ranar Talata a kusa da garuruwan Auga-Akoko-Ibilo da ke kan iyakan jihohin Ondo da Edo.

Yadda masu garkuwa da mutane suka tsere suka bar wadanda suka sace a daji
Yadda masu garkuwa da mutane suka tsere suka bar wadanda suka sace a daji. Hoto daga The Nation
Asali: Twitter

An gano su ne a wani daji da ke Ibilo a jihar Edo.

DUBA WANNAN: JAMB: Jihohi 5 da ke kan gaba wajen magudin jarabawar 2020

Mai magana da yawun rundunar sojoji ta 32 Artillery Brigade a Akure, Kyaftin Ayorinde ya ce tawagar sojoji da wasu jamian tsaro ne suka ceto sojan ba tare da an biya kudin fansa.

A wani rahoton, mun kawo muku cewa Rundunar Yan sanda ta jihar Sokoto ta kama mutum 155 daga karfe 8 na daren ranar Laraba zuwa karfe 6 na ranar Alhamis da suka saba dokar kulle da aka saka a jihar don dakile yaduwar annobar COVID-19.

Wannan na cikin wata sanarwa ce ta mai magana da yawun rundunar, Muhammad Sadiq, mai mukamin mataimakin superintendent na yan sanda ya fitar a ranar Alhamis a Sokoto kamar yadda Premium Times ta ruwaito.

Mr Sadiq ya ce twagar hadin gwiwa ta jamian tsaro karkashin jagorancin kwamishinan Yan sandan jihar, Ibrahim Kaoje, daga ranar 5 ga watan Mayu zuwa 14 ga watan Mayu ta kama motoci da babura a kalla 63.

Ya ce, "An gudanar da ingattacen binciken a kan kamen da aka yi kamar yadda kwamishinan yan sanda ya bayar da umurni kafin a kai su kotu."

Ya bayyana cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wurin kama duk wani mutum ko kungiya ta aka samu da saba dokar ta hana fita.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164