Da duminsa: Gwamnan Gombe ya janye dokar hana Sallar Jam'i, ya ce a bude Masallatai

Da duminsa: Gwamnan Gombe ya janye dokar hana Sallar Jam'i, ya ce a bude Masallatai

Gwamnatin jihar Gombe karkashin jagoranicin gwamna Inuwa Yahaya ta sanar da janye dokar hana ayyukan ibada a jam'i da aka kakaba domin takaita yaduwar cutar Coronavirus a jihar.

Za ku tuna cewa a ranar Laraba, 22 ga Afrilu, gwamnatin jihar Gombe ta kafa dokar hana bude cibiyoyin ibada a fadin jihar domin takaita yaduwar cutar Korona.

Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya ya bada umurnin ne na dokar hana fita a kananan hukumomin jihar 11 daga karfe 6 na yamma zuwa na safe.

Amma a yanzu, gwamnan ya ce za'a a iya bude wuraren ibada d sharadin za a yi rika bada tazara da juna.

Ya sanar da hakan ne bayan ganawarsa da shugabannin addinin jihar a gidan gwamnati a ranar Alhamis, 14 ga Mayu, 2020.

Ya ce dokar hana fitan da gwamnatin jihar ta sanya ya baya ta haifi 'da mai ido saboda ya taimaka wajen takaita yaduwar cutar.

A cewarsa, shugabannin addinin sun bada tabbacin cewa za su bi dukkan umurnin da hukumar hana yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta gindaya yayinda bude Masallatai da coci-coci.

Gwamnan ya umurci kwamitin yaki da cutar Koronan jihar ta horar da mamabobin kungiyoyin agajin addinai kan sharruda.

KU KARANTA: Adadin 'yan ta'addan da dakarun Najeriya suka halaka a daren jiya - Rundunar soji

Da duminsa: Gwamnan Gombe ya janye dokar hana Sallar Jam'i, ya ce a bude Masallatai
Da duminsa: Gwamnan Gombe
Asali: Twitter

A bangare guda, Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya amince da dakatar da dokar hana zirga - zirga da kulle jihar Borno sakamakon bullar annobar korona.

Ya janye dokar ne biyo bayan samun gagarumar nasarar da jihar ta yi a bangaren yaki da nnobar korona.

Mataimakin gwamnan Borno, Umar Kadafur, wanda shine shugaban kwamitin kar ta kwana a kan yaki da annobar a jihar, shine yasanar da hakan a cikin wani jawabi da ya fitar a daren ranar Laraba a Maiduguri.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng