Yanzu-yanzu: Allah ya yi wa kwamishina rasuwa a Oyo

Yanzu-yanzu: Allah ya yi wa kwamishina rasuwa a Oyo

Kwamishinan Muhalli da Albarkatun kasa na jihar Oyo, Mr Kehinde Ayoola ya rasu.

Ya rasu yana da shekaru 55 a duniya.

Ayoola, tsohon kakakin majalisar jihar ta Oyo, ya yi fama da rashin lafiya na kimanin sati biyu.

Ya rasu ne a wani asibiti mai zaman kansa a Iyaganku a garin Ibadan inda ake masa magani.

Dan siyasan haifafar garin Oyo ya wakilci mazabar Oyo ta Gabas daga shekarar 1999 and 2003.

Yanzu-yanzu: Allah ya yi wa kwamishina rasuwa a Oyo
Yanzu-yanzu: Allah ya yi wa kwamishina rasuwa a Oyo
Asali: UGC

DUBA WANNAN: Buhari ya nada sabon shugaban NALDA

An haifi Ayoola ne a ranar 14 ga watan Janairu a garin Oyo na jihar Oyo.

Ya yi karatun digir a Jamiar Obafemi Awolowo da ke Ile Ife.

Ya yi karatun nazarin kimiyyar dabobi da kula da muhalli.

Ya auri Olukemi, mataimakiyar Farfesa a tsangayar nazarin aikin noma.

Kuma suna da yara biyu.

Taiwo Adisa, mai magana da yawun gwamnan jihar Oyo Rotimi Makinde shima ya tabbatar da rasuwar kwamishinan.

Ba a tabbatar da cutar da ta yi sanadin rasuwarsa ba a lokacin hada wannan rahoton kamar yadda The Nation ta ruwaito.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164