Satar shanu: Kansilar da ake nema ruwa a jallo ya shiga hannu

Satar shanu: Kansilar da ake nema ruwa a jallo ya shiga hannu

Wakana Enan Ngari, Kansilar da ake nema ruwa a jallo a kan zargin satar shanu da wasu laifufuka a jihar Adamawa ya mika kansa hannun Yan sanda a karamar hukumar Numan na jihar.

DSP Suleiman Nguroje, Mai magana da yawun rundunar yan sanda na Adamawa ne ya bayyana wa manema labarai hakan a ranar Alhamis a Yola kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Nguroje ya ce an tafi da kansilar da ake zargi zuwa sashin binciken manyan laifuka na rundunar (CID) domin cigaba da bincike.

Satar shanu: Kansilar da ake nema ruwa a jallo ya shiga hannu
Satar shanu: Kansilar da ake nema ruwa a jallo ya shiga hannu. Hoto daga Sahara Reporters
Asali: UGC

DUBA WANNAN: Akwai yiwuwar har abada duniya ba za ta rabu da coronavirus ba - WHO

Nguroje ya ce, "Rundunar yan sandan jihar Adamawa tana son sanar da alumma cewa Kansila mai wakiltan mazabar Vulpi a karamar hukumar Numan ya mika kansa ga yan sanda.

"A baya gwamnatin jihar Adamawa ta fitar da sanarwar neman kansilar ruwa a jallo sakamakon zargin da ake yi na cewa yana da hannu wurin aikata wasu laifuka.

"Ya mika kansa ga Yan sanda a Numan kuma tuni an mika shi ga sashin binciken manyan laifuka (CID) domin bincike."

Kakakin yan sandan ya kuma ce ya jiyo kwamishinan yan sandan jihar, Mr Olugbenga Adeyanju yana kira ga alummar jihar musamman na Numan su kwantar da hankulansu su zauna lafiya.

Ya ce shugaban yan sandan ya bayar da tabbacin za a gudanar da bincike a kan wanda ake zargin kuma idan an same shi da laifi, rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba har sai an hukunta shi.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164