COVID-19: Tsohuwa mai shekaru 98 da warke daga korona a Legas

COVID-19: Tsohuwa mai shekaru 98 da warke daga korona a Legas

An sallami wata tsohuwa mai shekaru 98 da haihuwa daga cibiyar killace masu dauke da cutar COVID-19 a Legas bayan ta warke sarai.

Babajide Sanwo Olu, gwamnan jihar Legas ne ya sanar da hakan ta shafin Twitter a daren ranar Laraba.

Tana daya daga cikin mutane 26 da aka sallama a jihar ta Legas a ranar Laraba bayan an musu gwaji kuma sakamakon ya nuna sun warke.

DUBA WANNAN: COVID-19: Saudiyya za ta saka dokar kulle yayin hutun sallar Idi mai zuwa

Sakon da gwamnan ya wallafa a Twitter ya ce, "Yau, mun sallami wata tsohuwa mai shekaru 98, ita ce mai jinya mafi shekaru da muke da ita a Legas.

"An sallame ta tare da wasu majinyata 25, 13 maza yayin da 12 mata bayan gwajin da aka yi musu ya nuna sun warke daga cutar ta #COVID19, hakan ya kawo jimillar wadanda suka warke zuwa 528."

Sanwo Olu ya kuma mika godiyarsa ga maaikatan lafiya da sauran maaikatan da ke kan gaba wurin yaki da annobar a jihar.

Ya kuma yi kira da mutanen jihar su cigaba da kiyayye sharrudan da hukuma ke bayarwa domin kare kansu daga mummunar cutar.

A zuwa ranar 12 ga watan Mayun 2020, an tabbatar mutum 1,990 masu dauke da COVID-19 a jihar ta Legas adadin da ya dara na kowanne jiha a kasar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164