COVID-19: Saudiyya za ta saka dokar kulle yayin hutun sallar Idi mai zuwa

COVID-19: Saudiyya za ta saka dokar kulle yayin hutun sallar Idi mai zuwa

Saudiyya za ta saka dokar zaman gida na awa 24 a dukkan sassan kasar na tsawon kwanaki biyar yayin hutun karamar sallah wato Eid al-Fitr domin yaki da Covid19 kamar yadda Maaikatar harkokin cikin gida ta sanar a ranar Talata.

Masarautar da Saudiyya wacce a halin yanzu ta fitar da alkalluma mafi yawa na wadanda suka kamu da cutar a yankin Gulf tana iya kokarinta ne domin dakile yaduwar cutar.

Za a sake saka dokar hana fita baki daya daga ranar 23 zuwa 27 ga watan Mayu, kamar yadda sanarwar da maaikatar ta fitar a wani kafar watsa labarai na kasar.

Wannan lokacin ya yi dai dai da lokacin da alummar musulmi ke yi bikin Sallah bayan kammala azumin watan Ramadan.

COVID-19: Saudiyya za ta saka dokar kulle yayin hutun sallar Eid mai zuwa
COVID-19: Saudiyya za ta saka dokar kulle yayin hutun sallar Eid mai zuwa. Hoto daga Daily Trust
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: Dokar kulle a Kano: 'Yan sanda suna sintiri a Kasuwar Kwari

An saka dokar kulle a mafi yawancin sassan kasar bayan bullar cutar amma a watan da ta gabata gwamnatin ta sassauta dokar inda aka bawa mutane damar fita daga 9 na safe zuwa 5 na yamma.

An bawa shaguna da kantina umurnin budewa sai dai a wasu wurarren da mutane da yawa ke hada hada a birnin Makka da aka samu yawaitar masu cutar duk da dokar kullen.

Maaikatar Lafiya ta kasar a ranar Talata ta sanar da cewa adadin wadanda COVID-19 ta kashe a kasar sun kai 264 kuma wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar ya kai 42,925 yayin da wadanda suka warke sun kai 15,257.

A watan Maris, Saudiyya ta dage yin aikin Umrah saboda fargabar yaduwar annobar da corona a birnin na Makka mai tsarki.

Kawo yanzu, Mahukunta a kasar ba su riga sun sanar ko za a gudanar da aikin hajji ba a wannan shekarar da ake shirin yi a watan Yuli amma sun sanar da alummar musulmi su jinkirta da yin shirye shiryen aikin hajjin.

A shekarar 2O19, kimanin mutane miliyan 2.5 ne suka tafi kasar ta Saudiyya domin sauke farali da Allah ya wajabtawa musulmi masu hali a kalla sau daya a rayuwarsu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164