Buhari ya maye gurbin mamacin da ya nada mukami a gwamnatinsa

Buhari ya maye gurbin mamacin da ya nada mukami a gwamnatinsa

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya maye gurbin Tobias Okwuru, mamacin da ya nada a matsayin mamba a hukumar daidaito a rabon guraben aikin tarayya a tsakanin 'yan kasa (FCC) sati biyu da suka gabata.

Sunan marigayi Okwuru na daga cikin jerin sunayen mutane 37 da shugaba Buhari ya aikawa majlaisar dattijai domin amincewa da su a matsayin mambobin hukumar FCC.

Batun nadin mamaci a matsayin mamba a FCC ya jawo barkewar cece-kuce a tsakanin 'yan Najeriya.

A cikin wata wasika da shugaban majalisar dattijai, Ahmed Lawan, ya karanta a zauren majalisar ranar Talata, ya ce shugaba Buhari ya bukaci sauya sunayen mutane hudu da suka hada da Okwuru.

"Kamar yadda doka ta bani dama a sashe na 156(1) na kundin tsarin mulkin Najeriya na shekarar 1999, ina son sauya sunayen mutane hudu daga cikin sunayen mutanen da na aiko domin amincewa da su a matsayin mambobin hukumar FCC ," a cewar wasikar.

Sauran mutanen da shugaba Buhari ya maye sunayensu bayan marigayi Okwuru sune; Moses A (daga jihar Delta), Afamefuna Osi (daga jihar Ebonyi), Wasiu Kayode (daga jihar Legas) da Alakayi Mamman (daga jihar Nasarawa).

Buhari ya maye gurbin mamacin da ya nada mukami a gwamnatinsa
Buhari
Asali: Twitter

Bayan hakan, majalisar dattijai ta tabbatar da samun wasikar shugaban kasa, Muhammad Buhari, a kan neman amincewa da nadin Jumai Audi a matsayin shugabar hukumar NLRC (Nigerian Law Reform Commission).

Kazalika, shugaba Buhari ya nemi majalisar ta amince na nadin Ebele Chima, Bassey Abia, da Mohammed Ibraheem a matsayin kwamishinoni da zasu wakilcin yankunan da suka fito a hukumar NLRC.

DUBA WANNAN: Muhimman abubuwa 4 da gwamonin zasu tattauna yayin ganawarsu ranar Laraba

A wata wasikar da Buhari ya aikawa majalisar, ya nemi amincewarta da Diana Okonta (daga kudu maso kudu), Ya'ana Yaro (daga arewa maso gabas) a matsayin darektoci a hukumar NDIC (Nigeria Deposit Insurance Corporation).

Yahaya Abdullahi, barden majalisar dattijai, ya bukaci majalisar ta gaggauta amincewa da tabbatar da sunayen dukkan mutanen da shugaba Buhari ya aiko.

A ranar Litinin ne Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya amince da nadin Mohammed Bello Shehu, a matsayin sakataren hukumar kasafin kudaden haraji da gwamnatin tarayya ta samu.

Shehu, wanda nadinsa ya fara aiki a ranar 19 ga watan Maris, zai shafe zangon farko mai wa'adin shekaru biyar a hukumar RMAFC tare da zabin sabunta nadinsa a zango na biyu idan shugaban kasa ya ga dama.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: