Da duminsa: An sallami masu Coronavirus 22 a birnin Shehu bayan samun waraka

Da duminsa: An sallami masu Coronavirus 22 a birnin Shehu bayan samun waraka

Gwamnatin jihar Sokoto ta sanar da sallamar masu fama da cutar nan mai toshe numfashi watau Coronavirus 22 cikin 75 dake jinya a cibiyar killacewa dake unguwar Amanawa.

Shugaban kwamitin yaki da da cutar COVID19 na jihar, wanda shine kwamishanan lafiya, Dr Ali Inname, ya bayyana hakan yayinda yake hira da manema labarai a jihar ranar Talata.

Dr Inname ya ce mutane 106 ne suka kamu da cutar kawo ranar 11 ga Mayu 106 ne, kuma 12 sun rigamu gidan gaskiya.

Yace: "Daga cikin mutane 75 dake da cutar yanzu, mun samu nasarar sallaman mutane 22 da gwaji biyu daban-daban ya nuna sun waraka daga COVID-19."

"Jimillar wadanda aka sallama yanzu 41 cikin 106 da suka kamu da cutar a jihar."

"Bugu da kari, an samu karin wadanda suka mutu ya karu da daya yau."

Kwamishanan ya kara da cewa kashi 30% mata ne yayinda 70% maza ne.

Ya ce jihar ta bibiyi mutane 874 kuma an gwada 431 cikinsu.

A daren jiya, hukumar NCDC ta sanar da cewa ba'a samu kamuwar sabbin mutane da cutar Korona a jihar Sokoto ba amma jimillan masu cutar yanzu 106.

KU KARANTA: Da duminsa: Gwamnatin Kaduna ta sallami masu cutar Korona 12, 11 Almajirai ne

A daren jiya Litinin, an samu karin sabbin mutane 242 da suka kamu da cutar a Najeriya, kamar da hukumar NCDC ta sanar.

Kaow yanzu, mutane 4641 ne ya tabbata sun kamu da cutar a Najeriya. Yayinda 902 sun samu waraka kuma an sallamesu, 150 sun rigamu gidan gaskiya.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng