Yanzu-yanzu: Sabbin mutane 195 sun kamu da Coronavirus; Legas, Kano, Zamfara da Sokoto kekan gaba

Yanzu-yanzu: Sabbin mutane 195 sun kamu da Coronavirus; Legas, Kano, Zamfara da Sokoto kekan gaba

Cibiyar hana yaduwar cututtuka a Najeriya watau NCDC ta sanar da samun karin mutane 195 da suka kamu da cutar Coronavirus (#COVID19) a Najeriya a ranar Laraba, 6 ga Mayu, 2020.

Cibiyar ta bayyana hakan a shafin ra'ayinta na Tuwita inda tace: An samu karin mutane dari da tis'in da biyar (195) sun kamu da #COVID19. Yayinda 53 suka samu waraka, 5 sun mutu.

82-Lagos, 30-Kano, 19-Zamfara, 18-Sokoto, 10-Borno, 9-FCT, 8-Oyo, 5-Kebbi, 5-Gombe, 4-Ogun, 3 Katsina, 1-Kaduna, 1-Adamawa.

Jimilla:

Kamuwa: 3145

Sallama: 534

Mutuwa: 103

KU KARANTA: Matawalle ya nada madadin marigayi Sarkin Kauran Namoda

A yayin da likafar annobar korona ke ci gaba babu sassauci, wata kungiyar masu bincike a Jami'ar Fasaha ta Akure da ke jihar Ondo, ta yi wani bincike kan muhimmancin ta'ammali da wasu 'ya'yan itatuwa da kayan lambu masu bunkasa garkuwar jiki.

Sanadiyar yadda kawo yanzu ba a samar da maganin cutar korona ba, a halin yanzu dai ingatacciyar garkuwar jiki ita kadai ce ke iya yakar cutar a jikin mutum kamar yadda mahukuntan lafiya suka bayyana.

Kwararrun masanan na jami'ar FUTA sun bayar da sharawa a kan muhimmancin bunkasa garkuwa jiki ta hanyar ci da kuma shan wasu dangin 'ya'yan itatuwa da kayan lambu masu tarin sunadarai.

Jagoran masu binciken da ya kasance kwararren masani a fannin kimiya da fasahar abinci, Farfesa Ganiyu Oboh, ya ce kayan lambu da 'ya'yan itatuwa sun kunshi sunadarai masu bunkasa garkuwar jiki.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng