Katsina: An yanke wa dattijo dan shekara 70 da ya zazzagi Buhari hukunci

Katsina: An yanke wa dattijo dan shekara 70 da ya zazzagi Buhari hukunci

Wata kotu da ke zamanta a jihar Katsina a ranar Talata ya yanke wa wani mutum mai shekaru 70, Lawal Abdullahi Izala, hukuncin daurin watanni 18 a gidan gyaran hali.

An kama Izala ne a makon da ta gabata a kan zarginsa da zagin Shugaban kasa Muhammadu Buhari da Gwamna Aminu Masari na jihar Katsina kamar yadda Sahara Reporters ta ruwaito.

An gurfanar da dattijon da wasu mutane biyu a gaban kuliya a kan tuhumar furta kalaman da ka iya tayar da zaune tsaye da kuma rashin yi wa hukuma da a ta hanyar furta maganganu na cin mutunci.

Katsina: Kotu ta yanke wa dattijo dan shekara 70 da ya zazzagi Buhari hukunci
Katsina: Kotu ta yanke wa dattijo dan shekara 70 da ya zazzagi Buhari hukunci. Hoto daga Westafco
Asali: UGC

Da ya ke magana da manema labarai a ranar Talata, Izala ya ce ya yi furucin ne a cikin fushi lokacin da ya ziyarci kauyensu ya gano cewa yan bindiga sun kashe wasu yan uwansa sun kuma sace shanu 15.

DUBA WANNAN: Yanzu-yanzu: Dan majalisar jihar Borno ya rasu a asibiti

A yayin zartar da hukuncin, alkalin kotun ya ce an samu Izala da laifuka biyu na assasa fitina da rashin daa ga hukuma.

An yanke masa hukuncin daurin watanni shida a gidan gyaran hali na laifin farko sai kuma na shekara guda na laifi na biyu.

Sai dai an bawa Izala zabin biyan tara ta ₦10,000 na laifin farkon da kuma ₦20,000 na laifin na biyu.

Sahara Reporters ta ruwaito cewa wasu mutane masu tausayi a jihar sun biya wa dattijon kudin tarar da aka ci shi na ₦30,000.

An kuma saki dattijon ya koma gidansa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164