Yanzu-yanzu: Ganduje ya sassauta dokar kulle a Kano, ya sanar da ranakun walwala

Yanzu-yanzu: Ganduje ya sassauta dokar kulle a Kano, ya sanar da ranakun walwala

Gwamnan Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje ya sanar da sassauta dokar hana fita a jihar da Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya saka.

A cewar Ganduje, Mutane za su iya fita suyi walwala a ranakun Litinin da Alhamis daga karfe 10 na safe zuwa karfe 4 na yamma kamar yadda Sahara Reporters ta ruwaito.

Gwamnan ya bayyana cewa ba za a bude kasuwanni ba sai dai manyan kanti na sayar da kayayyakin masarufi.

Yanzu-yanzu: Ganduje ya sassauta dokar kulle a Kano, ya sanar da ranakun walwala
Yanzu-yanzu: Ganduje ya sassauta dokar kulle a Kano, ya sanar da ranakun walwala. Hoto daga Observers Times
Asali: UGC

DUBA WANNAN: Boko Haram: Shekau ya musanta rade-raden zai mika wuya, ya bada sharuddan sulhu

Ganduje ya kara da cewa Kasuwan Yankaba da na Yan Lamo kawai za a rika budewa a ranakun Litinin da Alhamis daga karfe 10 na safe zuwa karfe 4 na yamma.

Wannan na zuwa ne bayan matasa sun yi zanga zanga a birnin ta Kano inda suka koka kan dokar hana fitar.

Masu zanga zangar sun ce ba adalci bane a hana su fita kuma ba a samar musu da isasun kayan tallafi ba.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164