Yanzu-yanzu: Gobara ta lamushe shaguna masu yawa a garin Kaduna

Yanzu-yanzu: Gobara ta lamushe shaguna masu yawa a garin Kaduna

A kalla shaguna 20 wadanda suka hada da wurin siyar da magani ne suka babbake a jihar Kaduna.

Lamarin ya faru ne wurin karfe 7 na yamma a wurin Constitution road da ke babban birnin jihar.

Har a halin yanzu ba a san musabbabin gobarar ba, gidan talabijin din Channels ne ya wallafa.

A yayin da ake fitar da wannan rahoton, jami'an hukumar kwana-kwana da sauran masu taimakon gaggawa duk basu isa wurin ba.

Amma kuma, mazauna yankin tare da masu wucewa ne ke kokarin kashe gobarar.

Hakazalika, babu daya daga cikin masu shagunan da ke kusa saboda dokar hana zirga-zirgar da gwamnatin jihar ta saka don yaki da cutar COVID-19.

Yanzu-yanzu: Gobara ta lamushe shaguna masu yawa a garin Kaduna
Yanzu-yanzu: Gobara ta lamushe shaguna masu yawa a garin Kaduna
Asali: Twitter

KU KARANTA: COVID-19: Ganduje ya bayyana yadda cutar ke yaduwa a jihar Kano

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng