Da duminsa: Bankuna za su iya budewa a Legas, Abuja da Ogun

Da duminsa: Bankuna za su iya budewa a Legas, Abuja da Ogun

Kwamitin kar ta kwanan fadar shugaban kasa kan yaki da cutar COVID-19 ta ce rassan bankuna a jihar Legas, jihar Ogun da birnin tarayya Abuja za su iya fara budewa daga ranar Litnin, 4 ga Mayu.

Shugaban kwamitin, Sani Aliyu, ya ce za'a amince bankunan su bude daga karfe 8 na safe zuwa 2 na rana.

Sani ya kara da cewa ofisoshin ma'aikatun gwamnatin tarayya da kamfanoni da masana'antun masu kere-kere zasu iya budewa.

Zaku tuna cewa tun ranar 29 ga Maris, shugaba Muhammadu Buhari ya bada umurnin rufe dukkan masana'antu da ofisoshin gwamnati domin takaita yaduwar cutar Coronavirus.

Yace:"Za'a amince ma'aikatan gwamnati su koma bakin aiki daga ranar 4 ga Mayu amma ba dukkan ranakun mako za'a amince su fita ba kuma ba dukkan ma'aikata ba saboda rage cinkoso a ofisoshin."

"Za'a amince bakuna su bude amma za'a rage awannin budewa zuwa karfe 8 na safe zuwa 2 na rana tare da biyayya da lura da dukkan dokokin kare kai da na ambata a baya."

"Hakazalika za'a amince masu gina tituna masu muhimmanci su cigaba da aiki amma sai gwamnatocin jihohi sun basu dama."

Da duminsa: Bankuna za su iya budewa a Legas, Abuja da Ogun
Da duminsa: Bankuna za su iya budewa a Legas, Abuja da Ogun
Asali: UGC

KU KARANTA: Annobar covid-19 ta harbi sabbin mutane 195 a Najeriya, 38 a Kano

Gwamnatin jihar Legas ta sanar da sallamar majinyata 49 dake kwance a cibiyoyin killacewanta na muguwar cutar nan mai toshe numfashi watau Coronavirus (COVID19).

Gwamnan jihar, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana hakan ne a hirar da yakeyi yanzu haka da manema labarai a unguwar Marina ta jihar.

Ya ce 48 yan Najeriya ne yayinda 1 bature.

Hakazalika Ma'aikatar kiwon lafiyar jihar ta bayyana hakan a jawabin da ta sake a shafin na Tuwita inda tace mutanen 49 sun hada maza 21 da mata 28.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng