Kano: Shugaban masu rinjayen majalisar wakilai ya yi tsokaci a kan mace-mace

Kano: Shugaban masu rinjayen majalisar wakilai ya yi tsokaci a kan mace-mace

Alhassan Ado Doguwa, shugaban masu rinjaye na majalisar wakilan Najeriya, ya ce akwai yuwuwar mace-macen da ake yi a jihar Kano ya wuce rayukan da mayakan Boko Haram suka dauka a kasar nan, matukar ba a dauka mataki ba.

Doguwa, mai wakiltar Doguwa da Tudun Wada a majalisar wakilai, ya sanar da hakan ne a taron zauren majalisar na yau Talata yayin da yake mika bukatar kawo karshen mace-mace a jiharsa.

Jaridar The Cable ta ruwaito cewa, ana ta mace-mace a jihar Kano wacce ake dangantawa da annobar COVID-19.

Dan majalisar ya ce daga abinda ke faruwa a jihar Kano, lamarin ba na tashin hankali bane, har da alhini.

Ya ce akwai bukatar aikin gaggawa don ceto jihar. Akwai bukatar 'yan majalisar su gaggauta kawo karshen mace-macen tare da dakile hakan daga zuwa wani wuri.

"Ina tsoron yadda lamurra ke tafiya a jihar Kano. Idan ba a dauka mataki ba, akwai yuwuwar barnar da za ta faru ta fi ta Boko Haram muni," yace.

Kano: Shugaban masu rinjayen majalisar wakilai ya yi tsokaci a kan mace-mace
Kano: Shugaban masu rinjayen majalisar wakilai ya yi tsokaci a kan mace-mace
Asali: Twitter

KU KARANTA: COVID-19: Martanin jama'ar jihar Kano a kan hukuncin Buhari

"Boko Haram na kisa ne ta hanyar amfani da bindiga da fushi. Wannan kuwa na kashe jama'a ne a hankali ta hanyar wawurewa da rage yawansu.

"Ballantana a tsakiyar birnin Kano inda akwai a kalla akwatunan zabe 600. Mutanen nan na dankare ne a wuri daya ba tare da wani rarrabewa ba." yace.

Shugaban majalisar ya kara da cewa wannan ba abu bako bane a jihar ballantana a yayin lokacin rani. Amma wannan na da matukar firgitarwa.

"A baya, mun saba samun irin wannan mace-macen ne a yayin rani amma abinda muke gani yanzu ya fi karfin hankali," yace.

A ranar Litinin ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bada umarnin garkame jihar na makonni biyu yayin da ake bincikar sanadin mace-macen.

Kamar yadda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana, zai gaggauta daukan matakai don shawo kan matsalar da jihar ta Kano ke ciki.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng