Yanzu-yanzu: Sabbin Mutane 87sun kamu da Coronavirus, 18 a Borno

Yanzu-yanzu: Sabbin Mutane 87sun kamu da Coronavirus, 18 a Borno

Cibiyar hana yaduwar cututtuka a Najeriya watau NCDC ta sanar da samun karin mutane 87 da suka kamu da cutar Coronavirus (#COVID19) a Najeriya a ranar Asabar, 25 ga Afrilu, 2020.

Cibiyar ta bayyana hakan a shafin ra'ayinta na Tuwita inda tace: “An samu karin mutane tamanin da bakwai(87) sun kamu da #COVID19"

33 a Lagos

18 a Borno

12 a Osun

9 a Katsina

4 a Kano

4 a Ekiti

3 a Edo

3 a Bauchi

1 a Imo

A daidai karfe 11:30 na 25 ga Afrilu, an tabbatar kamuwar mutane 1182 da cutar COVID-19 a Najeriya

An sallmi: 222

Mutuwa: 35

KU KARNATA: COVID-19: Budurwa roki NCDC ta kama mahaifiyarta saboda karya dokar zaman gida a Nasarawa

Kawo yanzu, ga jerin jihohin da cutar ta bulla da adadinsu:

Lagos-689

FCT-138

Kano-77

Ogun-35

Osun-32

Gombe-30

Katsina-30

Borno-30

Edo-22

Oyo-18

Kwara-11

Akwa Ibom-11

Bauchi-11

Kaduna-10

Ekiti-8

Ondo-4

Delta-6

Rivers-3

Jigawa-2

Enugu-2

Niger-2

Abia-2

Zamfara-2

Sokoto-2

Benue-1

Anambra-1

Adamawa-1

Plateau-1

Imo-1

A bangare guda, Allah ya yi wa tsohon babban alkalin kotun daukaka karar shari'ar Musulunci ta jihar Kano, Dahiru Rabiu rasuwa.

Ya rasu ne a yau Asabar a gidansa da ke kwatas din Galadanci a cikin garin Kano.

Daya daga cikin iyalan mamacin ne ya sanar wa jaridar Leadership. Ya ce za a kai mamacin makwancinsa a yau bayan an kammala tanadin addinin Musulunci a kan gawar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel