Yanzu-yanzu: Sabbin Mutane 87sun kamu da Coronavirus, 18 a Borno

Yanzu-yanzu: Sabbin Mutane 87sun kamu da Coronavirus, 18 a Borno

Cibiyar hana yaduwar cututtuka a Najeriya watau NCDC ta sanar da samun karin mutane 87 da suka kamu da cutar Coronavirus (#COVID19) a Najeriya a ranar Asabar, 25 ga Afrilu, 2020.

Cibiyar ta bayyana hakan a shafin ra'ayinta na Tuwita inda tace: “An samu karin mutane tamanin da bakwai(87) sun kamu da #COVID19"

33 a Lagos

18 a Borno

12 a Osun

9 a Katsina

4 a Kano

4 a Ekiti

3 a Edo

3 a Bauchi

1 a Imo

A daidai karfe 11:30 na 25 ga Afrilu, an tabbatar kamuwar mutane 1182 da cutar COVID-19 a Najeriya

An sallmi: 222

Mutuwa: 35

KU KARNATA: COVID-19: Budurwa roki NCDC ta kama mahaifiyarta saboda karya dokar zaman gida a Nasarawa

Kawo yanzu, ga jerin jihohin da cutar ta bulla da adadinsu:

Lagos-689

FCT-138

Kano-77

Ogun-35

Osun-32

Gombe-30

Katsina-30

Borno-30

Edo-22

Oyo-18

Kwara-11

Akwa Ibom-11

Bauchi-11

Kaduna-10

Ekiti-8

Ondo-4

Delta-6

Rivers-3

Jigawa-2

Enugu-2

Niger-2

Abia-2

Zamfara-2

Sokoto-2

Benue-1

Anambra-1

Adamawa-1

Plateau-1

Imo-1

A bangare guda, Allah ya yi wa tsohon babban alkalin kotun daukaka karar shari'ar Musulunci ta jihar Kano, Dahiru Rabiu rasuwa.

Ya rasu ne a yau Asabar a gidansa da ke kwatas din Galadanci a cikin garin Kano.

Daya daga cikin iyalan mamacin ne ya sanar wa jaridar Leadership. Ya ce za a kai mamacin makwancinsa a yau bayan an kammala tanadin addinin Musulunci a kan gawar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng