COVID-19: Ma'aikatan Lafiya bakwai sun kamu da Korona a Borno

COVID-19: Ma'aikatan Lafiya bakwai sun kamu da Korona a Borno

– Ma'aikatan Lafiya guda bakwai a jihar Borno sun kamu da kwayar cutar COVID-19

– Kwamishinan Lafiya na jihar, Kwaya-Bura ne ya bayyana hakan a ranar Jumaa a garin Maiduguri

– Kwamishinan ya ce mutum 15 ne suka kamu da cutar a jihar inda biyu cikinsu sun riga mu gidan gaskiya

Kwamishinan Lafiya na jihar Borno, Salihu Kwaya Bura ya ce ma'aikatan lafiya bakwai a jihar sun kamu da kwayar cutar COVID-19 da ake fi sani da coronavirus.

Kwaya-Bura wanda kuma shine sakataren kwamitin kar ta kwana na yaki da annobar Korona a jihar ya bayyana hakan ne a ranar Jumaa a Maiduguri yayin da ya ke bayar da bayani a kan annobar a jihar.

Ya ce mutane 15 ne suka kamu da cutar a jihar kawo yanzu sannan mutum biyu sun mutu.

COVID-19: Ma'aikatan Lafiya bakwai sun kamu da Korona a Borno
COVID-19: Ma'aikatan Lafiya bakwai sun kamu da Korona a Borno
Asali: Facebook

DUBA WANNAN: Kasashe 10 da aka fi samun masu dauke da cutar COVID-19

"An binciko wadanda suka yi cudanya da wandanda suka kamu da cutar kuma ana sa ido a kansu domin ganin halin da suke ciki.

"Mutane sun ankarar da mu game da mutane tara da ake zargin sun kamu, mun yi bincike a kansu, bakwai cikinsu ba su da alamomin cutar amma muna cigaba da bincike a kan biyu," in ji Kwaya-Bura.

Ya jinjinawa al'ummar jihar bisa hakuri da sadaukarwarsu a rana da biyu bayan saka dokar kullen inda ya ce kwamitin kar ka kwanan tana shirin yin sausauci ga dokar don albarkacin watan Ramadana.

Kwaya-Bura ya ce, "Muna son mu ga yadda za mu bari masu sayar da kankara, kosai da shayi da biredi su fara yin sanaarsu a gundumominsu domin mutane su rika saya lokacin shan ruwa."

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164