Yanzu-Yanzu: Covid-19 ta hallaka mutane 2 a Legas

Yanzu-Yanzu: Covid-19 ta hallaka mutane 2 a Legas

An sake samun mutuwar wasu mutane biyu a jihar Legas a sanadiyar cutar Coronavirus.

Kwamishinan Lafiya na jihar, Farfesa Akin Abayomi, shi ne ya tabbatar da wannan rahoto da ya wallafa a kan shafinsa na sada zumunta a ranar Alhamis.

Farfesa Abayomi ya ce a ranar Laraba an sake samun sabbin mutane 74 wanda cutar corona ta harba, inda jimillar masu dauke da cutar ya kai 512 a jihar.

Kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Twitter, Abayomi ya ce "an samu karin mutane 74 wanda cutar coronavirus ta harba a jihar a ranar Laraba, 22 ga Afrilu, 2020."

"Jimillar masu dauke da cutar a jihar sun kai 512."

"Jimillar wadanda cutar Coronavirus ta hallaka a jihar sun kai 18."

KARANTA KUMA: Gwamnatin Lebanon ta nuna bacin rai kan dan kasarta da ke neman sayar da wata 'yar Najeriya

A yayin da hukumomin lafiya ke ci gaba da aiki tukuru babu dare babu rana domin hana yaduwar cutar coronavirus a Najeriya, cutar tamkar wutar daji na ci gaba da bazuwa a kasar.

A halin yanzu an samu bullar cutar covid-19 a jihohi 26 na Najeriya ciki har da babban birnin tarayya kamar yadda alkaluman cibiyar dakile yaduwar cututtuka a kasar NCDC suka tabbatar.

Taswirar NCDC a ranar Laraba, 22 ga watan Afrilun 2020, ta ce cutar corona ta harbi mutane 873 a Najeriya yayin da tuni mutane 197 suka warke daga cutar.

Ya zuwa yanzu dai mutane 28 cutar ta hallaka a duk fadin Najeriya kamar yadda kididdigar alkaluman ta tabbatar.

Babu shakka jihar Legas ce a kan sahu na gaba ta fuskar yawan mutane da cutar ta harba, sai kuma birnin Abuja a mataki na biyu yayin da jihar Kano ta biyo bayansu.

Taskar bayanai ta Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta tabbatar cewa jimillar mutane da cutar ta harba a fadin duniya ta kai 2,639,243 yayin da mutane 183,820 suka riga mu gidan gaskiya.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng