Yanzu-yanzu: An sallami mutum 1 da ya warke daga cutar Covid-19 a Kaduna

Yanzu-yanzu: An sallami mutum 1 da ya warke daga cutar Covid-19 a Kaduna

Kwamishinan lafiya ta jihar Kaduna ta sanar da sallamar karin mutum daya wanda ya warke daga cutar Covid-19 a jihar.

Wannan ya kai jimillar wadanda aka sallama a jihar zuwa biyar tun bayan na ranar 14 ga watan Afirilun 2020.

Ta tabbatar da cewa an sake samun wasu mutum 3 da suka kamu da cutar, dukkansu kuwa sun dawo daga tafiye-tafiye ne.

Kamar yadda takardar da ministar ta fitar ta bayyana, "Sun hada da wani matashi mai shekaru 23 wanda ya dawo daga Istanbul bayan ya biyo ta Dubai.

"Dattijo mai shekaru 51 wanda aka gwada a Samaru da ke karamar hukumar Sabon Gari sai kuma wani mai shekaru 42 da ke Unguwan Geza a Kaduna."

Takardar ta kara da cewa, "Wannan sabbin mutanen da suka dauko cutar ta hanyar fita jihar na bayyana hatsarin da ke tattare da yawo zuwa wata jiha a cikin kasar nan.

"Wadannan tafiye-tafiyen na da matukar hatsari saboda ta hanyarsu ne ake kwaso cutar a kaita inda babu.

"A don haka ma'aikatar lafiya ta jihar Kaduna ke kara kira ga jama'ar jihar da su zauna a gida tare da kauracewa tafiye-tafiye don gudun yaduwar annobar."

Yanzu-yanzu: An sallami mutum 1 da ya warke daga cutar Covid-19 a Kaduna
Yanzu-yanzu: An sallami mutum 1 da ya warke daga cutar Covid-19 a Kaduna
Asali: UGC

KU KARANTA: Da duminsa: An dakatar da gwajin Covid-19 a jihar Kano

Ma'aikatar lafiyar ta sake tunatar da jama'a amfanin wanke hannu da tsafta don gudun yada kwayar cutar.

A wani labari na daban, Legit.nga ta ruwaito cewa an dakatar da gwajin kwayar cutar Covid-19 a jihar Kano sakamakon rashin kayan aikin.

Farfesa Sadiq Isah na kwamitin yaki da cutar Covid-19 a Kano ya tabbatar wa da BBC hakan a ranar Laraba.

Ya ce dole ne yasa suka yi hakan don babu sinadaran gwajin kwayar cutar don ci gaba da gwajin a jihar.

Farfesan ya ce a halin yanzu, za a dinga kai samfurin da aka diba na wadanda ake zargin suna dauke da cutar har babban birnin tarayyar Abuja.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng