COVID-19: Titunan Kano bayan dokar hana zirga-zirga ta fara aiki (Hotuna)
- A safiyar yau Juma'a, manyan tituna da na cikin anguwanni a jihar Kano sun bayyana kamar an sharesu
- Wannan ya biyo bayan dokar hana zirga-zirga da gwamna Ganduje ya kafa a jihar don gujewa yaduwar muguwar cutar coronavirus a jihar
- Amma kuma an ga tsirarun mutane sun kafa kungiya daban-daban a cikin anguwanni inda suke tattauna a kan dokar hana zirga-zirgar
A safiyar yau Juma'a, manyan tituna da na cikin anguwanni a jihar Kano sun bayyana kamar an sharesu.

Asali: Facebook
Wannan ya biyo bayan dokar hana zirga-zirga da gwamna Ganduje ya kafa a jihar don gujewa yaduwar muguwar cutar coronavirus a jihar.

Asali: Facebook
Jaridar The Nation ta ruwaito cewa mazauna jihar sun yi biyayya ga dokar don kuwa babu mutane ko ababen hawa a titunan.

Asali: Twitter
An tsananta tsaro ta hanyar baza jami'an tsaro a wurare daban-daban don tabbatar da cewa an bi dokar.
Amma kuma an ga tsirarun mutane sun kafa kungiya daban-daban a cikin anguwanni inda suke tattaunawa a kan dokar hana zirga-zirgar.

Asali: Facebook
Ababen hawan jami'an tsaro ne kadai aka bari suke kaiwa da kawowa sai kuma masu ayyuka na musamman a jihar.

Asali: Twitter
KU KARANTA: Jawabi mai ratsa zuciya da Buratai yayi wa dakarun Najeriya da ke Borno
A ranar Talata ne mai girma gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya bada umarnin rufe jihar na mako daya.
Dokar hana shige da fice a jihar Kano din za ta fara aiki ne daga ranar Alhamis, 16 ga watan Afirilun 2020.
Kamar yadda mai bada shawara ta musamman ga gwamnan ya wallafa, ana sa ran dokar hana shige da ficen za ta yi aiki ne mako daya cif kafin a ga abinda hali yayi.
A tsawon lokacin, ba a bukatar kaiwa da kawowar jama'a ko ababen hawa a jihar. Gwamnan ya tabbatar da cewa jami'an tsaro za su damke duk wanda aka kama da laifin take dokar.

Asali: Twitter

Asali: Twitter
Wannan dokar ta biyo bayan samun mutane hudu masu dauke da cutar coronavirus da aka yi a jihar Kano.
A wani labari na daban, Legit.ng ta wallafa cewa gwamnatin jihar Kano, karkashin jagorancin Gwamna Abdullahi Ganduje ta ce za ta rufe wasu daga cikin kasuwannin da ke jihar tare da tsananta dokar hana shiga da fice a kan iyakokinta.

Asali: Twitter
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng