Tsaro: Rundunar sojin Najeriya ta samu sabbin makaman zamani don yaki da Boko Haram

Tsaro: Rundunar sojin Najeriya ta samu sabbin makaman zamani don yaki da Boko Haram

- Rundunar sojin Najeriya ta zaburo don yakar 'yan ta'addan Boko Haram a yankin Arewa maso gabas din kasar nan

- Rundunar ta karo makaman yaki na zamani don yakar 'yan ta'addan

- An gano cewa, sabbin ababen hawan na yaki na daga cikin kashin farko na makaman da kasar nan ta siya a kasar China

Gwamnatin kasar China ta ce kashi na farko na ababen hawan yaki da rundunar sojin Najeriya ta siya a kasar sun iso Najeriya.

Kamar yadda jaridar Ukdefencejournal ta ruwaito, ababen hawan sun hada da tankokin yaki masu kirar VT-4 da wasu ababen hawan biyu masu tuka kansu.

Rundunar sojin ta yi wannan siyayyar gaggawar ne daga hannun gwamnatin kasar China din a matsayin sabon salo na tsananta yaki da ta'addanci a yankin arewacin Najeriya.

Laftanal Janar Lamidi Adeosun, shugaban tsari na rundunar sojin, ya ce wannan kwangilar an sa hannu a kanta tsakanin Najeriya da NORINCO tun a 2019.

Dakarun sojin da ake tsammanin za su yi amfani da ababen hawan na yaki, an horar dasu tuni a kasar China.

Gwamnatin kasar China ta kara da cewa, kasar Najeriya ce ta farko a yankin nahiyar Afrika da ta fara mallakar irin wadannan tankokin yakin na zamani.

Tsaro: Rundunar sojin Najeriya ta samu makaman zamani don yaki da Boko Haram
Tsaro: Rundunar sojin Najeriya ta samu makaman zamani don yaki da Boko Haram
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: COVID-19: Hotunan yadda dan kamfai na mata ya zama takunkumin rufe fuska a Kenya

A wani labari na daban, 'yan gudun hijira 14 ne aka tabbatar da mutuwarsu yayin da 15 daga ciki suka samu raunika daban-daban.

Hakan ya faru ne sakamakon barkewar gobara a sansanin 'yan gudun hijarar da ke karamar hukumar Ngala ta jihar Borno.

Kamar yadda jaridar Daily Trust ta bayyana, gobarar ta fara ne da karfe 2:15 na yammacin ranar Alhamis a sansanin. Kamar yadda wata majiya ta tabbatar, an yi kokari wajen kashe wutar da gaggawa.

"A halin yanzu, ranar 16 ga watan Afirilun 2020, gobara ta kama a sansanin 'yan dudun hijira da ke Ngala. Gobarar ta lashe gidaje 1250 amma ba a tabbatar ba," majiyar ta ce.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164