An samu karin masu cutar Coronavirus 11 a Najeriya, jimilla 373

An samu karin masu cutar Coronavirus 11 a Najeriya, jimilla 373

Cibiyar Takaita Yaduwar Cututtuka ta Najeriya, NCDC, a jiya ta tabbatar da sabbin mutane 3O da suka kamu da coronavirus a kasar wadda hakan ya kawo jimillar masu cutar a kasar zuwa 373.

Mutum 11 ne kuma cutar ya kashe a kasar a halin yanzu.

A cewar hukumar ta NCDC, "Kawo yanzu an tabbatar da masu cutar 373, 99 sun warke an sallame su yayin da mutane 11 sun mutu sakamakon cutar a Najeriya."

A baya, NCDC ta ruwaito cewa an samu karin mutane 19 da suka kamu da cutar a jihohi biyar

14 a Lagos

2 a Abuja

1 a Kano

1 a Akwa Ibom

1 a Edo

Daga bisani bayan karfe 11 na daren Talata ta sake ruwaito wa cewa, "an samu karin mutum 11 masu cutar a jihar Legas."

DUBA WANNAN: Shekau ya saki sabon sakon murya a kan maganin coronavirus

Sakon da hukumar ta wallafa a shafinta na Twitter ya ce,"

“A karfe 11:OO na daren 14 ga Afrilu, mutane 373 suka kamu da COVID19 a Najeriya. 99 sun warke, kuma 11 sun mutu.“

"A karfe 11 na daren 14 ga watan Afrilu, an samu bullar cutar #COVID19 a jihohi 19 da birnin tarayya."

Hukumar ta bayar da kididdigan masu cutar a jihohin Najeriya kamar haka

Legas - 214

Osun - 2O

Edo - 15

Oyo - 11

Ogun - 9

Bauchi - 6

Kaduna - 6

Akwa Ibom - 6

Katsina - 5

Kwara - 4

Kano - 4

Ondo - 3

Delta - 3

Enugu - 2

Ekiti - 2

Rivers - 2

Benue - 1

Niger - 1

Anambra - 1

Ta kara da cewa hukumar tana daukan matakan da suka dace domin dakile yaduwar cutar a kasar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164