Zamfara: Rundunar 'yan sandan ta samu kwaryar jini a gidan matsafi

Zamfara: Rundunar 'yan sandan ta samu kwaryar jini a gidan matsafi

- Rundunar 'yan sandan jihar Zamfara ta gano kwarya mai cike da jini a gidan wani da ake zargi da zama dan kungiyar asiri a Gusau

- A makon da ya gabata ne Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya ruwaito cewa gidan 'yan kungiyar asirin na nan a kwatas din Dallatu

- A yayin samamen, 'yan sandan sun samu kayayyakin tsafin da suka hada da kwarya mai cike da jini sai kuma sunayen wasu manyan 'yan siyasar jihar a rubuce a wata takardar

Rundunar 'yan sandan jihar Zamfara ta gano kwarya mai cike da jini a gidan wani da ake zargi da zama dan kungiyar asiri a Gusau, babban birnin jihar.

Jami'in hulda da jama'a na rundunar, Mohammed Shehu ya bayyana wa manema labarai a ranar Asabar.

A makon da ya gabata ne Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya ruwaito cewa gidan 'yan kungiyar asirin na nan a kwatas din Dallatu da ke kusa da sabuwar tashar mita a Gusau.

'Yan sandan sun kai samame ne sakamakon ayyukan laifin da aka gano ana aikatawa a gidan.

Ya ce wadanda suka kai bayanan sun ce mazauna yankin sun gano cewa duk lokacin da matsafan suka shiga gidan, dukkan kananan halittu kamar sh kadangaru da kiyashi na mutuwa.

Zamfara: Rundunar 'yan sandan ta kama kwaryar jini a gidan matsafi
Zamfara: Rundunar 'yan sandan ta kama kwaryar jini a gidan matsafi
Asali: UGC

KU KARANTA: Boko Haram: Buratai ya koma Arewa maso gabas har sai ta'addanci ya kare

A yayin samamen, 'yan sandan sun samu kayayyakin tsafin da suka hada da kwarya mai cike da jini, sai kuma sunayen wasu manyan 'yan siyasar jihar a rubuce a wata takardar.

Shehu ya ce an dauka samfurin jinin da aka tarar a kwaryar don tantancewa a dakin bincike.

An gano cewa jinin dan Adam ne da ke rukunin O. Ya ce ana ci gaba da bincike a kan lamarin a halin yanzu.

Jami'in hulda da jama'ar ya ce, a halin yanzu dai an kama wasu wadanda ake zargi da hannu a ciki.

Rundunar 'yan sandan ta bayyana cewa za ta sanar da jama'a abinda bincike ya nuna, jaridar Daily Trust ta wallafa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng