Coronavirus a Najeriya: Manyan abubuwa 20 da suka faru

Coronavirus a Najeriya: Manyan abubuwa 20 da suka faru

Bisa lissafin cibiyar takaita yaduwar cuta a Najeriya NCDC ta wallafa, kawo yanzu mutane 276 suka kamu da cutar ta Coronavirus a Najeriya.

Yayinda 44 sun warke, sun samu lafiya kuma an sallamesu, 6 sun rigamu gidan gaskiya.

Jihar Legas ke kan gaba da mutane 145, sai Abuja 54, sannan Osun 20.

Ga jerin abubuwa 20 da suka faru:

1. Ranar 27 ga Febrairu 2020 aka samu bullar cutar a Najeriya.

2. Ranar 9 ga Maris shugaba Buhari ya nada kwamitin kar ta kwana na yakar cutar karkashin jagorancin Sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha.

3. Ranar 18 ga Maris: An hana jirage daga wasu kasashe 11 shigowa Najeriya. Sun hada da Amurka, Ingila, Jamus, Norway, Sin, Dss.

4. Ranar 20 ga Maris: An kulle filayen jirgin saman Kano, Enugu, da Fatakwal.

5. Ranar 21 ga Maris: An kulle filin jirgin saman Legas da Abuja.

6. Ranar 23 ga Maris: Gwamnatin tarayya ta rufe dukkan iyakokin Najeriya na tsawon makonni hudu.

7. Ranar 24 ga Maris: Shugaban maaikatan fadar shugaban kasa, Abba Kyari, da gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed, suka kamu da cutar Coronavirus.

8. Ranar 24 ga Maris: Majalisar wakilan tarayya sun samar da dokar tallafawa yan Najeriya.

9. Ranar 24 ga Maris: An hana wasu maaikata da yan jarida da dama shiga fadar shugaban kasa.

10. Ranar 26 ga Maris: Gwamnatin tarayya ta baiwa gwamnatin Legas tukwicin bilyan goma don yakar cutar.

KU KARANTA Ba zamu baiwa Likitocin China hadin kai ba - Kungiyar Likitocin Najeriya

11. Ranar 26 ga Maris: Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa tana neman mutane 4,370 da sukayi mu'amala da wasu da aka tabbatar sun kamu.

12. Ranar 27 ga Maris: Shugaba Buhari ya baiwa cibiyar NCDC N15bn da suka bukata.

13. Ranar 27 ga Maris: Ministan Abuja ya bada umurnin kulle makarantun Abuja da kasuwanni.

14. Ranar 28 ga Maris: Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya kamu da cutar.

15. Ranar 29 ga Maris: Shugaba Buhari ya yi jawabi ga yan Najeriya, ya sanar da dokar rufe Abuja, Legas da Ogun na tsaon makkoni biyu.

16. Ranar 29 ga Maris: Kwantrola Janar na hukumar shiga da fice, Mohammed Babandede, ya kamu da cutar Coronavirus.

17. Ranar 30 ga Maris: Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya kamu da cutar Coronavirus.

18. Ranar 6 ga Afrilu: Buhari ya nemi bashin N2.53 Tiriliyan daga bankin duniya da IMF domin kawar da yiwuwar shiga matsin tattalin arziki.

19. Ranar 8 ga Afrilu: Gwamnatin tarayya ta kaddamar da na'urar numfashi da ruwan feshi da aka kera a Najeriya.

20. Ranar 8 ga Afrilu: Likitoci daga kasar Sin sun dira Najeriya domin taimakawa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng