Yanzu-yanzu: An samu sabbin mutum 22 da suka kamu da Coronavirus a Najeriya

Yanzu-yanzu: An samu sabbin mutum 22 da suka kamu da Coronavirus a Najeriya

Hukumar Kula da Cututtuka masu yaduwa ta Najeriya (NCDC) ta tabbatar da samun karin mutane 22 da suka kamu da kwayar cutar COVID-19 a kasar.

Hakan na nuna cewa jimillar wadanda suka kamu cutar a kasar ya kai 276.

A cewar hukumar ta NCDC sabbin wadanda suka kamu da cutar an samu 15 ne a Legas, hudu a birnin tarayya Abuja, biyu a jihar Bauchi, sai kuma guda daya a jihar Edo.

Hukumar ta bayyana hakan ne a shafin ta na Twitter mai lakabin @NCDCgov kamar yadda ta saba.

DUBA WANNAN: Coronavirus: Dole 'yan Najeriya su yi watsi da addini - Guru Maharaj Ji

A wani rahoton, kun ji cewa a ranar Alhamis 9 ga watan Maris ne gwamnatin tarayya za ta fara sakin fursunonin da shugaban Buhari ya yi wa afuwa ta musamman a yunkurin ta na rage cinkoso a gidajen na gyaran hali a kasar.

Jaridar Leadership ta gano cewa za a fara sakin fursunonin ne bayan amincewar shugaban kasa Buhari da bukatar da ministan harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola ya gabatar masa don rake cinkoso a gidajen yarin.

Gwamnatin tarayyar ta Najeriya ta dauki wannan matakin ne don rage yaduwar kwayar cutar coronavirus a kasar.

Wannan sakon na cikin wata takardar gayyata ne da ofishin ministan ta aike wa manema labarai na gayyatar su taro a hedkwatan hukumar kula da gidajen gyaran hali na kasa, NCoS.

Kakakin hukumar da NCoS, DCC A.C. Njoku ne ya saka hannu a kan sakon.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164