Za mu fara gwajin maganin COVID-19 a Legas - Farfesa Abayomi

Za mu fara gwajin maganin COVID-19 a Legas - Farfesa Abayomi

- Kwamishinan Lafiya na jihar Legas, Farfesa Akin Abayomi ya ce jihar tana shirin fara yin gwajin maganin coronavirus

- Kwamishinan ya ce za a fara gwajin ne a kan wasu majinyata da ke jihar da kuma ma'aikatan hukumarsa da nufin samo tabbatacen maganin cutar

- A halin yanzu dai kasashen duniya da ke fama da cutar sun fara gudanar da gwaje-gwaje masu kama da wannan da nufin samo maganin

Kwamishinan Lafiya na jihar Legas Farfesa Akin Abayomi ya ce jihar ta gama shirye-shiryen fara gwajin maganin COVID-19 a kan majiyanta a jihar tare da hadin gwiwar Cibiyar kawar da cututtuka masu yaduwa ta Najeriya (NCDC) da wasu hukumomin.

Kwamishinan ya bayyana hakan ne yayin wata jawabi da ya yi a ranar Litinin kamar yadda The Punch ta ruwaito.

Za a fara gwajin maganin COVID-19 a Legas - Farfesa Abayomi
Za a fara gwajin maganin COVID-19 a Legas - Farfesa Abayomi
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: Labari da dumi-dumi: Tsohon malamin da ya koyar da Abacha, Dr Habibu Gwarzo ya rasu a Kano

Ya ce, "Ana gudanar da bincike masu yawa a kasashen duniya, saboda haka akwai yiwuwar nan da wani lokaci a gaba za mu samu abinda za mu iya kira takamamme maganin COVID-19. Za mu fara yin namu gwaje-gwajen a Legas tare da wasu hukumomi da NCDC kuma muna fatan sati mai zuwa za mu fara gwada magungunan a kan wasu majinyata da ma'aikatan mu a Legas.

"Muna da wurin gwajin kwayar cutar guda uku a Legas kuma muna sa ran za mu bude wasu sabbi a wasu wuraren a jihar. Guda ukun da muke da su a yanzu sun hada da Lagos State Biobank da ke asibitin Yaba, Sashin binciken kwayoyin hallita na Virus a asibitin koyarwa na jami'ar Legas da kuma Cibiyar Binciken Lafiya na kasa a Legas."

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel