Yanzu-yanzu: Masu cutar Coronavirus 6 sun gudu da inda aka killacesu a Osun

Yanzu-yanzu: Masu cutar Coronavirus 6 sun gudu da inda aka killacesu a Osun

Gwamnatin jihar Osun ta alanta neman mutane shida masu cutar Coronavirus ruwa a jallo bayan sun gudu daga inda aka killacesu a Ejigbo, jihar Osun ranar Juma'a.

Mutanen na cikin tawagar matafiyan da suke shigo Najeriya daga kasar Cote d'ivoire a makon da ya gabata kuma aka samesu da cutar ta COVID-19.

A lokacin gwamnatin jihar ta killacesu a kauyen Ejigbo.

Wani jawabi daga gwamnatin jihar ya bayyana sunayen mutane shidan da lambar wayarsu.

KU KARANTA: An gano mai coronavirus da ya tsere daga asibiti a Osun

Yanzu-yanzu: Masu cutar Coronavirus 6 sun gudu da inda aka killacesu a Osun
killacesu a Osun
Asali: Twitter

A bangare guda, Hukumar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta sanar da cewa an samu karin mutane ashirin (20) da suka kamu da cutar Coronavirus (#COVID19) a Najeriya a ranar Juma'a, 3 ga Afrilu, 2020.

Hukumar ta bayyana hakan a shafin ra'ayinta na Tuwita ranar Juma'a inda tace: “An tabbatar da mutane ashirin (20) sun kamu da #COVID19 a Najerya, 11 a Legas, 3 a Abuja, 3 a Edo, 2 a Osun, 1 a Ondo.“

"An samu karin mutane biyu da mutu; 1 a Legas, 1 a Edo."

“Dai-dai Karfe 10:30 na daren 3 ga Afrilu, mutane 210 aka tabbatar sun kamu da COVID19 a Najeriya, an sallami 25 , kuma hudu ya rigamu gidan gaskiya.“

Lagos- 109

Abuja - 41

Osun- 21

Oyo- 8

Akwa Ibom- 5

Ogun- 4

Edo- 6

Kaduna- 4

Bauchi- 3

Enugu- 2

Ekiti- 2

Rivers-1

Benue- 1

Ondo - 1

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng