Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 20 a Najeriya

Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 20 a Najeriya

Hukumar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta sanar da cewa an samu karin mutane ashirin (20) da suka kamu da cutar Coronavirus (#COVID19) a Najeriya a ranar Juma'a, 3 ga Afrilu, 2020.

Hukumar ta bayyana hakan a shafin ra'ayinta na Tuwita ranar Juma'a inda tace: “An tabbatar da mutane ashirin (20) sun kamu da #COVID19 a Najerya, 11 a Legas, 3 a Abuja, 3 a Edo, 2 a Osun, 1 a Ondo.“

"An samu karin mutane biyu da mutu; 1 a Legas, 1 a Edo."

“Dai-dai Karfe 10:30 na daren 3 ga Afrilu, mutane 210 aka tabbatar sun kamu da COVID19 a Najeriya, an sallami 25 , kuma hudu ya rigamu gidan gaskiya.“

KU KARANTA: Cibiyar NCDC ta saki lambobin jiha-jiha da mutum zai iya kira

Lagos- 109

Abuja - 41

Osun- 21

Oyo- 8

Akwa Ibom- 5

Ogun- 4

Edo- 6

Kaduna- 4

Bauchi- 3

Enugu- 2

Ekiti- 2

Rivers-1

Benue- 1

Ondo - 1

KU KARANTA: An sake sallaman mutane 4 bayan sun warke daga cutar Coronavirus

Mutumi mai shekaru 55 a duniya da ya mutu a asibitin koyarwan jami'ar jihar Legas LUTH, Idi Araba, sakamakon cutar Coronavirus bai fadawa ma'aikatan kiwon lafiya gaskiyar abinda yake fama da shi ba lokacin da aka kai shi asibiti.

Majiya a asibitin ya bayyana cewa sai bayan mutuwarsa aka gudanar da gwaji aka gano cewa yana dauke da cutar Coronavirus a jikinsa.

Hakazalika masu jinyarsa suka ki bayyanawa asibitin ainihin abinda ke damunsa da kuma irin tafiye-tafiyen da yayi zuwa kasar waje a makonni baya-bayan nan.

"Amma bayan mai rijistan asibitin ya bayyana masa abubuwan da suka gano a jikinsa, mutumin ya bayyana gaskiyar cewa lallai da yiwuwan ya kamu da cutar COVID-19 saboda tafiyar da yayi kasar waje."

"Ya bayyana cewa tun lokacin da ya dawo daga kasar Holan makonni biyu da suka shude yake fama da tari." Cewar majiyar

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng