Cibiyar NCDC ta saki lambobin jiha-jiha da mutum zai iya kira

Cibiyar NCDC ta saki lambobin jiha-jiha da mutum zai iya kira

Cibiyar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta saki jerin lambobin jiha-jiha da mutum zai iya kira idan ya bukaci magana ko gwaji.

Cibiyar ta jaddada cewa cutar COVID-19 ba ta yawo a iska. Innama kasa take fadi idan mai dauke da cutar yayi atishawa ko tari.

Saboda haka, ta shawarci mutane su rika nisanta da juna na akalla tsawon mita biyu.

Cibiyar NCDC ta saki lambobin jiha-jiha da mutum zai iya kira
Cibiyar NCDC ta saki lambobin jiha-jiha da mutum zai iya kira
Asali: Facebook

KU KARANTA: Bayan rufe iyakokin jiha, Yan sanda na karban cin hancin N500 hannun matafiya - Gwamnatin Ayade

A bangare guda, yaduwar cututtuka ta Najeriya (NCDC), ya nuna cewa an sake samun karin sabbin mutane 23 da suka kamu da cutar coronavirus a kasar.

A wani rubutu da ta wallafa a shafinta na Twitter, hukumar ta ce tara daga cikin mutanen sun kasance a jahar Lagas ne, bakwai daga Abuja inda biyar suka fito daga jihar Akwa Ibom sai kuma mutum daya daga jahar Bauchi.

Yanzu haka jumullar mutane da ke dauke da cutar a kasar sun zama 174, an salami mutane tara yayinda biyu suka mutu.

Lagos- 91

FCT- 35

Osun- 14

Oyo- 8

Ogun- 4

Edo- 4

Kaduna- 4

Bauchi- 3

Enugu- 2

Ekiti- 2

Rivers-1

Benue- 1

Akwa Ibom- 5

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel