Coronavirus: Mutane biyu da suka kamu a Kaduna na kusa da El-Rufa'i ne - Gwamnatin jihar

Coronavirus: Mutane biyu da suka kamu a Kaduna na kusa da El-Rufa'i ne - Gwamnatin jihar

Kwamishanan kiwon lafiyan jihar Kaduna, Dakta Amina Baloni, ta tabbatar da cewa lallai mutane biyun da suka kamu da cutar Coronavirus a Kaduna wadanda suka hadu da El-Rufa'i ne. The Nation ta ruwaito.

Mun kawo muku rahoton cewa cibiyar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC a ranar Litinin ya alanta cewa an samu karin mutane biyu da suka kamu da Coronavirus a Kaduna.

Hakazalika a ranar 28 ga Maris, gwamnan jihar Kaduna, Nasiru El-Rufa'i, ya zama mutum na farko da ya kamu da cutar Coronavirus a jihar.

A jawabin da Balori ta saki ranar Talata a Kaduna, ta ce jami'an kiwon lafiyan jihar na bibiyan wadanda suka hadu da gwamnan domin takaita yaduwar.

Ta yi kira ga mazaunan jihar su bi umurnin gwamnati suyi zamansu a gida domin takaita yaduwar annobar.

Coronavirus: Mutane biyu da suka kamu a Kaduna na kusa da El-Rufa'i ne - Gwamnatin jihar
Coronavirus: Mutane biyu da suka kamu a Kaduna na kusa da El-Rufa'i ne - Gwamnatin jihar
Asali: Facebook

Hukumar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta sanar da cewa an samu karuwar mutane ashirin da suka kamu da cutar Coronavirus (#COVID19) a Najeriya.

Hukumar ta bayyana hakan a shafin raayinta na Tuwita ranar Litinin inda tace: “An tabbatar da mutane ashirin sun kamu da #COVID19 a Najerya. 13 a Legas, 2 a Abuja, 2 a Kaduna, .“

“Dai-dai Karfe 9:o0 na daren 30 ga Maris, mutane 131 aka tabbatar sun kamu da COVID19 a Najeriya, an sallami takwas, kuma biyu ya rigamu gidan gaskiya.“

Ga jerin jiha-jiha

Lagos- 81

FCT- 25

Ogun- 3

Enugu- 2

Ekiti- 1

Oyo- 8

Edo- 2

Bauchi- 2

Osun-2

Rivers-1

Benue- 1

Kaduna- 3

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel