Coronavirus: Mutane biyu da suka kamu a Kaduna na kusa da El-Rufa'i ne - Gwamnatin jihar

Coronavirus: Mutane biyu da suka kamu a Kaduna na kusa da El-Rufa'i ne - Gwamnatin jihar

Kwamishanan kiwon lafiyan jihar Kaduna, Dakta Amina Baloni, ta tabbatar da cewa lallai mutane biyun da suka kamu da cutar Coronavirus a Kaduna wadanda suka hadu da El-Rufa'i ne. The Nation ta ruwaito.

Mun kawo muku rahoton cewa cibiyar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC a ranar Litinin ya alanta cewa an samu karin mutane biyu da suka kamu da Coronavirus a Kaduna.

Hakazalika a ranar 28 ga Maris, gwamnan jihar Kaduna, Nasiru El-Rufa'i, ya zama mutum na farko da ya kamu da cutar Coronavirus a jihar.

A jawabin da Balori ta saki ranar Talata a Kaduna, ta ce jami'an kiwon lafiyan jihar na bibiyan wadanda suka hadu da gwamnan domin takaita yaduwar.

Ta yi kira ga mazaunan jihar su bi umurnin gwamnati suyi zamansu a gida domin takaita yaduwar annobar.

Coronavirus: Mutane biyu da suka kamu a Kaduna na kusa da El-Rufa'i ne - Gwamnatin jihar
Coronavirus: Mutane biyu da suka kamu a Kaduna na kusa da El-Rufa'i ne - Gwamnatin jihar
Asali: Facebook

Hukumar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta sanar da cewa an samu karuwar mutane ashirin da suka kamu da cutar Coronavirus (#COVID19) a Najeriya.

Hukumar ta bayyana hakan a shafin raayinta na Tuwita ranar Litinin inda tace: “An tabbatar da mutane ashirin sun kamu da #COVID19 a Najerya. 13 a Legas, 2 a Abuja, 2 a Kaduna, .“

“Dai-dai Karfe 9:o0 na daren 30 ga Maris, mutane 131 aka tabbatar sun kamu da COVID19 a Najeriya, an sallami takwas, kuma biyu ya rigamu gidan gaskiya.“

Ga jerin jiha-jiha

Lagos- 81

FCT- 25

Ogun- 3

Enugu- 2

Ekiti- 1

Oyo- 8

Edo- 2

Bauchi- 2

Osun-2

Rivers-1

Benue- 1

Kaduna- 3

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng