Majalisar Dattijai za ta tafi hutu saboda Coronavirus

Majalisar Dattijai za ta tafi hutu saboda Coronavirus

Majalisar Dattawan Najeriya tana zama na musamman domin shirye-shiryen dakatar da zamanta na wani lokaci.

Rahotanni sun bayyana cewa dakatar da zaman ya zama dole ne domin kare yaɗuwar ƙwayar Coronavirus (COVID-19)

A cewar hadimin daya daga cikin shugabannin majalisar, "Majalisar ba ta da zabi sai dai dakatar da zamanta a yau."

Majalisar Dattijai za ta tafi hutu saboda Coronavirus
Majalisar Dattijai za ta tafi hutu saboda Coronavirus
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: Yanzu-yanzu: Abba Kyari ya kamu da Coronavirus

A makon da ya gabata ne majalisar da dakatar da ziyara zuwa harabar da kuma tarukan jin ra'ayin mutane.

A wani rahoton, kun ji cewa sakamakon gwajin da aka yi wa Shugaba Muhammadu Buhari na Covid-19 ya nuna cewa shugaban baya dauke da kwayar cutar kamar yadda The Cable ta ruwaito.

Hukumar NCDC ta sanar da shugaban kasar cewa ba ya dauke da kwayar cutar a safiyar yau a Abuja.

A cewar wata majiya daga fadar shugaban kasa, gwajin da aka yi ya nuna cewa shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, Abba Kyari ya kamu da cutar kamar yadda sakamakon ya nuna a ranar Litinin.

Kyari ya tafi Jamus a ranar Asabar 7 ga watan Maris inda ya gana da wasu jami'an kamfanin Siemens a binrin Munich a kan shirin fadada aikin wutan lantarki a Najeriya.

Tuni dai shugaban ma'akatan fadar shugaban kasar ya killace kansa domin kada ya yada cutar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164