Coronavirus: Limaman Abuja sun goyi bayan Sultan kan rufe masallatai

Coronavirus: Limaman Abuja sun goyi bayan Sultan kan rufe masallatai

- Kwamitin Limaman masallatai na babban birnin tarayya Abuja sun goyi bayan sarkin Musulmi, Abubakar Sa'ad III kan matakin rufe masallatai

- Limaman sun ce an dauki matakin ne domin kare yaduwar annobar cutar Coronavirus da a halin yanzu ta ke yaduwa a kasashen duniya

- Limaman sun shawarci al'umma su rika yin sallar jam'i a gidajensu da iyalansu ko wuraren aikinsu tare da adadin mutane kalilan

Kwamitin Limaman masallatai a babban birnin tarayyar Najeriya Abuja (CFII) sun goyi bayan shugaban kwamitin koli na harkokin addinin musulunci (NSCIA) a kasar, Sultan Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar III game da umurnin da ya bayar na rufe masallacin kasa da ke Abuja da sauran masallatai da ke birnin tarayyar.

Coronavirus: Limaman masallatai na Abuja son goyi bayan Sultan kan rufe masallatai
Coronavirus: Limaman masallatai na Abuja son goyi bayan Sultan kan rufe masallatai
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: Yanzu-yanzu: Buhari bai kamu da Covid-19 ba, Abba Kyari ya kamu

Kwamitin, a cikin sanarwar da ta fitar a ranar Litinin mai dauke da sa hannun Sakataren ta, Ishaq Y. Zango ta ce an dauki matakin ne bayan tuntubar masu ruwa da tsaki a fanin da suka hada da likitoci da wasu manyan limamai da malamai, Grand Muftee Na Najeriya, Sheikh Sherif Ibrahim Saleh da shugabannin NSCIA.

Zango ya ce, "Muna goyon bayan kiraye-kirayen da ake yi na dakatar da yin sallar jam'i na taron jama'a masu yawa a dukkan masallatai da wuraren da ake sallah, ko da sallar Juma'a ce ko kuma sallolin farilla biyar na kowanne rana ko kuma rufe masallacin a inda akwai bukatar hakan domin kiyaye yaɗuwar mummunar annobar da ta fado wa al'umman duniya baki daya na ƙwayar cutar Covid-19 da aka fi sani da Coronavirus.

"Za mu iya yin Sallah ta jam'i tare da iyalan mu ko kuma tare da mutane kadan a gidajen mu ko ofisoshin mu", in ji Zango.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164