Yanzu-yanzu: Za a hana sallar Juma'a da taron coci na ranar Lahadi a Legas saboda Coronavirus

Yanzu-yanzu: Za a hana sallar Juma'a da taron coci na ranar Lahadi a Legas saboda Coronavirus

Gwamnatin jihar Legas ta ce za ta bukaci shugabannin musulmi da na kirista a jihar su dakatar da yin sallar Juma'a a masallatai da kuma taron ibadah na ranar Lahadi a coci a jihar domin kare yiwuwar yaduwar coronavirus.

Kwamishinan labarai na jihar, Mista Gbenga Omotosha ne ya bayar da wannan sanarwar yayin da ya ke magana da manema labarai a ranar Laraba jim kadan bayan an tabbatar da sabin mutane biyar na dauke da kwayar cutar a jihar.

Yanzu-yanzu: Za a hana sallar Juma'a da taron coci na ranar Lahadi a Legas saboda Coronavirus
Yanzu-yanzu: Za a hana sallar Juma'a da taron coci na ranar Lahadi a Legas saboda Coronavirus
Asali: UGC

DUBA WANNAN: Budurwa ta sa an damke mutumin da ya taba mata nono a motar haya

Ya ce, "Mun san cewa gwamnatin tarayya ta umurci hukumar kula da matasa masu yi wa kasa hidima (NYSC) ta rufe sansanoninta. A ranar Talata, kwamishinan harkokin cikin gida ya ce za a gudanar da taro da shugabannin addinai.

"Za mu ba su shawarar cewa a dakatar da yin sallar Juma'a da ibadah na ranar Lahadi a duk wurin da mutane da yawa ke taruwa.

"Duba da yadda lamara ke tafiya a yanzu, ina da tabbacin cewa za a basu shawarar su dakatar da yin ibadan cikin taron mutane domin kiyaye lafiyar mu baki daya. Ina da tabbacin za su amince da hakan."

A wani rahoton, mun kawo muku cewa gwamnonin yankin Arewa maso yamma sun sanar da cewa za a rufe dukkan makarantu da ke yankin na tsawon kwanaki 30 kamar yadda The Nation ta ruwaito.

A cikin sakon bayan taro da gwamnonin suka fitar ta bakin shugaban kungiyar gwamnonin yankin, Gwamna Aminu Masari na jihar Katsina, sun ce ya zama dole a dauki matakin hakan domin kare yaduwar cutar da Coronavirus a yankin.

An samu samu bullar wata cuta da ake zargin coronavirus ne a jihar ta Katsina a karo na farko a ranar Laraba.

Gwamanonin sun yi taro na a Kaduna domin bita kan kallubalen tsaro da ke adabar yankin.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel