Dalilin da yasa na ziyarci Buhari - Diri

Dalilin da yasa na ziyarci Buhari - Diri

- Gwamnan jihar Bayelsa, Mista Diri Douye ya kai wa Shugaba Muhammadu Buhari ziyara a fadarsa ta Aso Rock da ke babban birnin tarayya Abuja

- Wannan dai shine karo na farko da gwamnan na jam'iyyar PDP ya ke ziyarar shugaban kasar tun bayan da ya kama mulki a watan Fabrairun 2020

- Gwamna Diri Douye ya ce ya ziyarci shugaban kasar ne domin ya gabatar da kansa kuma ya sanar da shi cewa a shirye ya ke ya yi aiki da gwamnatin tarayya domin kawo cigaba da zaman lafiya a jiharsa

Gwamnan jihar Bayelsa, Diri Douye a ranar Talata ya ce ya kai wa Shugaban kasa Muhammadu Buhari ziyara ne domin ya gabatar da kan shi ga shugaban kasar a hukumance.

Douye ya yi bayanin cewa tun lokacin da ya kama aiki a matsayin gwamna a ranar 14 ga watan Fabrairun 2020 jiya (Talata) ce karo na farko da ya ziyarci shugaban kasar a fadarsa ra Aso Villa da ke babban birnin tarayya, Abuja.

Dalilin da yasa na ziyarci Buhari - Diri
Dalilin da yasa na ziyarci Buhari - Diri
Asali: UGC

DUBA WANNAN: Budurwa ta sa an damke mutumin da ya taba mata nono a motar haya

Bayan kammala taronsa da shugaban kasa misalin karfe 1.39 na rana, ya shaidawa manema labarai na gidan gwamnati cewa a shirye ya ke ya yi aiki tare da gwamnatin tarayya domin tabbatar da zaman lafiya a jiharsa.

Idan ba a manta ba Duoye ya zama gwamnan Bayelsa ne bayan hukuncin kotun koli na kasa a ranar 13 ga watan Fabrairun 2020 da aka soke zababbun 'yan takarar gwamna na jam'iyyar All Progressives Congress (APC), Mista David Lyon da mataimakinsa awanni 24 kafin a ranstar da shi.

Gwamnan ya ce, "Tunda na fara aiki a matsayin gwamnan jihar Bayelsa, ban zo na gaishe da uban kasa ba. A yau, gashi na aikata hakan; na zo na ziyarci uban kasar mu kuma domin muyi aiki tare da gwamnatin tarayya domin tabbatar da zaman lafiya da cigaba mai dorewa a jiha ta. Wannan shine dalilin da yasa na ziyarci shugaban kasa a yau."

A wani rahoton, kun ji cewa shugaba Buhari ya amince da dage bikin wasanni na kasa (NSF) da aka yi wa lakabi da Edo 2020 a matsayin wani mataki na kare yaduwar cutar Coronavirus a kasar.

Ministan Wasanni na Najeriya Sunday Dare ya sanar da cewa za a dage wasanni na kasar da aka shirya yi a Birnin Benin na jihar Edo.

'Yan wasa a dukkan jihohin kasar sun dade suna shirin zuwa Birnin Benin domin hallartar wannan wasannin kafin sanarwar ta fito a ranar Talata 17 ga watan Maris.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164