An hana masu shayi, yan babur, masu suya wuce karfe 11 na dare a Sokoto

An hana masu shayi, yan babur, masu suya wuce karfe 11 na dare a Sokoto

A ranar Litinin, hukumar yan sanda a jihar Sokoto ta alanta hana hawa babur da keke a daidaita sahu a jihar daga karfe 11 na dare zuwa 6 na safe.

Kakakin hukumar yan sandan jihar, ASP Mohammed Sadiq Abubakar, ya bayyana hakan ne a jawabin da ya saki madadin kwamishanan yan sandan jihar, Ibrahim Sani Kaoje.

A cewarsa, hukumar ta dau wannan matakin ne domin samun cigaba wajen nasarorin da ake samu wajen yakan fashi da makami, garkuwa da mutane, da hare-haren yan bindiga a jihar.

Ya kara da cewa dukkan masu shayi da sayar da Suya su rife dandalinsu fari daga karfe 11 na dare zuwa 6 na safe.

Wakilin Vanguard ya ziyarci teburan masu shayi da Suya domin tabbatar da yadda mutane ke biyayya ga sanarwar kuma ya bayyana cewa lallai mutane sun yi biyayya.

A hira da wani mai shago, yace ”Na samu labarin dokar kuma ba zan yarda a kamani ba, ka san yadda yan sandanmu suke, suna son amfani da kowace dama.”

An hana masu shayi, yan babur, masu suya wuce karfe 11 na dare a Sokoto
An hana masu shayi, yan babur, masu suya wuce karfe 11 na dare a Sokoto
Source: UGC

Za ku tuna cewa a ranar 20 ga watan Janairu ne gwamnatin jihar ta haramta amfani da babura da daddare a jihar. Ta ce an dauki matakin ne domin inganta tsaro a jihar.

Wasu daga cikin mutane da suka bayyana ra'ayoyinsu sun ce dokar tana janyo musu wahalhalu domin babura suke amfani da shi don zirga-zirga a jihar.

Wani mai sanaar achaba Yusif Mohammed ya ce "Kudin da na ke samu ya ragu sosai saboda galibi da daddare na ke aikin jigilar fasinja da kayayyaki.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng