Sanusi II zai yi limancin sallar Juma'a a Awe
An fara shirye-shirye domin tsohon Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya yi limancin sallar Juma'a a garin Awe.
Wata majiya kwaƙwara ta shaidawa Daily Trust cewa an shirye-shirye domin bawa Sanusi limancin sallar Juma'a duk sati a garin.
Masallacin Juma'ar tana hade ne da fadar Sarkin Awe, Alhaji Isa Abubakar Umar.

Asali: UGC
DUBA WANNAN: Sarkin Loko ya bayyana abinda suka tattauna da Sanusi II a daren da ya kwana a garinsa
Matasa sun fara tururuwa zuwa masallacin dauke da taburma da dadduma domin hallartar sallar ta Juma'a.
Idan ba manta ba tsohon Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II shine ya ke limancin sallar Juma'a a Kano kafin a lokacin da ya ke sarauta.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng