Idan mijina baya gamsar dani fita zanyi na nemi maza a titi - Juliet Njemanze
Fitacciyar jarumar fina-finan kudancin Najeriya Nollywood ta bayyana cewa matukar abokin rayuwarta baya gamsar da ita a bangaren jima'i to lallai babu yadda ta iya illa ta fita taci amanarshi
Jarumar ta bayyana hakane a wata hira da tayi da Vanguard.
A cewarta ko da za a bata duka kudin duniya, amma kuma bata gamsuwa a fannin jima'i to tabbas babu abinda zai hanata cin amanar abokin rayuwarta.
"A wajena banda bautar ubangiji babu abinda ya kai jima'i muhimmanci. Dole ya zama yana da kwazo a gado. Tabbas a wajena jima'i yafi kudi, saboda zaka bani duka kudin duniyar nan, amma idan baka gamsar dani dole zan fita na ci amanarka," cewar ta.

Asali: Facebook
Sai dai kuma Njemanze ta ce ba za ta iya yin fim din batsa ba, saboda imanin da take da shi na addini, amma kuma za ta yi rungume-rungume sama-sama.
"Akwai abubuwan da ba zan iya yi ba a fim, idan har abinda za a sanya ni nayi a fim ya sabawa koyarwar addinina ba zan yadda nayi ba. Ba zan iya yin fim din batsa ba.
KU KARANTA: Rikici ya barke wajen rabon gado bayan matar mamacin ta gano cewa mijinta yayi auren sirri kafin ya mutu
"Zan iya fitowa nayi rungume-rungume a fim, amma ba zan iya zina a ciki ba. Ina matukar jin imani na a jikina. Ina son Allah, kuma ina karanta Bible ina addu'a."
Juliet Njemenze an haifeta a cikin garin Kano, tayi suna a harkar fim ne bayan ta fito a cikin fim din Obi Emenloye mai suna 'Calabash'.
Haka kuma ta fito a cikin fina-finai irin su 'Tears in my Heart', 'My Regret', 'Pharaoh Let My People Go', '15 Years of Slavery', 'My Friend My Pain', da kuma 'Avoidable Blunder'.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng