Yanzu-yanzu: Buhari da gwamnan Nasarawa suna ganawa a Aso Rock

Yanzu-yanzu: Buhari da gwamnan Nasarawa suna ganawa a Aso Rock

Shugaban kasa Muhammadu Buhari da gwamnan jihar Nasarawa, Mista Abdullahi Sule suna ganawa a halin yanzu.

Gwmana Sule ya iso fadar Aso Rock ne misalin karfe 10 na safe gabanin taron majalisar zartarwa na kasa da za a gudanar kamar yadda The Punch ta ruwaito.

A halin yanzu dai ba a san abinda gwamnan zai tattauna ba a ganawarsa da Shugaba Buhari.

Yanzu-yanzu: Buhari da gwamnan Nasarawa suna ganawa a Aso Rock
Yanzu-yanzu: Buhari da gwamnan Nasarawa suna ganawa a Aso Rock
Asali: UGC

DUBA WANNAN: Kauyen Loko: Muhimman abubuwa 7 da ya kamata a sani game da masaukin Sanusi na farko

Jihar Nasarawa ce inda aka bawa tsohon sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II masauki a ranar Litinin bayan gwamnatin jihar Kano ta cire shi daga kujerar mulkin Kano.

Wata majiyar ta ce akwai yiwuwar gwamnan ya ziyarci shugaban kasar ne domin ya bashi bayani a kan halin tsaro da jihar ke ciki a halin yanzu.

A wani rahoton, mun kawo muku cewa gwamnatin jihar Kaduna ta ba Muhammadu Sanusi II gurbin aiki bayan tube masa rawani da gwamnatin jihar Kano tayi a ranar Litinin.

Ta bashi gurbi ne a KADIPA, cibiyar habaka kasuwancin jihar. A wata takarda da ta fito daga gidan Kashim Ibrahim, Gwamna Nasir El-Rufai ya amince da kafa shugabannin cibiyar KADIPA din.

An kafa cibiyar ne a 2015 kuma tana kan gaba ne wajen habaka kasuwancin jihar tare da saukakawa kasuwanci a jihar Kaduna.

Sanarwar da mai bawa gwamna shawara a fanin watsa labarai, Muyiwa Adekeye ya aike wa Premium Times a ranar Talata ta ce, “Malam Nasir El-Rufai ya amince da zaben mai martaba, Muhammadu Sanusi II zuwa shugabancin KADIPA."

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164