Da duminsa: Coronavirus ta bulla a kasar Kamaru

Da duminsa: Coronavirus ta bulla a kasar Kamaru

Kasar Kamaru ta tabbatar da bullar sabuwar cutar Coronavirus a kasar sanadiyar wani dan kasan Faransa da ya shiga Yaounde, babbar birnin kasar ranar 24 ga Febrairu, gwamnatin ta sanar ranar Juma'a.

Tuni an killace Baturen, dan shekara 58 a asibiti, ma'aikatar kiwon lafiyan kasar suka sanar.

Mun kawo muku a baya cewa Kasar Tunisiya da kasar Senegal sun tabbatar da bullar cutar Coronavirus na farko, hakan ya ya kai adadin kasashen da ta bulla a nahiyar Afrika biyar.

Gabanin shigarta kasashen nan biyu a yau Litinin, kasashen Misra, Algeria, da Najeriya sun tabbatar da bullar cutar da ta hallaka akalla mutane 3000 a fadin duniya.

A wani hira da manema labarai da ministan kiwon lafiyan kasar Senegal, ya shirya a birnin Dakar ranar Litinin, ya bayyana cewa wani dan kasan Faransa ya shigo da cutar kasar.

A kasar Tunisiya kuwa, wani dan kasar Italiya ne ya jajubo musu cutar.

Da duminsa: Coronavirus ta bulla a kasar Kamaru
Da duminsa: Coronavirus ta bulla a kasar Kamaru
Asali: Facebook

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng